Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa Za Ta Bada Lamunin Sama Da Naira Biliyan 3 Ga Hukumar Alhazan Jihar

Published

on

Majalisar zartaswa ta jihar Jigawa ta amince da bukatar hukumar Alhazai ta jihar na naira biliyan uku da miliyan dari uku da sittin a matsayin lamuni daga gwamnatin jihar.

Kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu na jihar Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai, bayan kammala taron majalisar da aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse.

Ya bayyana cewa,  majalisar ta amince da hakan ne don bai wa hukumar damar ajiyar kujeru 400 na maniyyatan jihar Jigawa domin gudanar da ayyukin  Hajjin shekarar 2025.

A cewarsa, amincewar ta biyo bayan  gamsuwar da Majalisar ta yi, bisa yadda hukumar Alhazai ta Jiha ta mayar da bashin Naira biliyan biyu da miliyan dari biyu da gwamnatin ta bata a shekarar 2024.

Haka zalika Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce majalisar ta amince da shigar da dukkan masu rike da mukaman siyasa a cikin shirin kula da liyafa na jihar, kamar yadda hukumar kula da lafiya ta jihar Jigawa  JICHMA ta tanadar  a doka mai lamba. 02 -2024, da nufin inganta harkokin kiwon lafiya a jihar da ma Najeriya baki daya kamar yadda sakataren gwamnatin jihar ya gabatar.

Ya ce majalisar ta kuma bada goyon baya ga amincewar da Gwamna Umar Namadi ya yi, na sakin Naira Miliyan Dari Biyu da Hamsin a matsayin wani asusun hadin gwiwa da hukumar UNICEF domin siyan kayan abinci mai gina jiki ga kananan yara marasa lafiya.

Ya kara da cewa, amincewar kuma wani bangare ne na kokarin gwamnatin Namadi na yaki da matsalar rashin abinci mai gina jiki a tsakanin yara a jihar, kamar yadda ma’aikatar lafiya ta gabatar.

 

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai19 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara