Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda 96 daga gwamnatin tarayya.

Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Jihar da aka gudanar a Fadar Gwamnati da ke Dutse.

A cewarsa, majalisar ta amince da sayen gidajen ne daga Ma’aikatar Gidaje da Raya Birane ta Tarayya.

Ya bayyana cewa sayen gidajen na da nufin magance matsalar matsuguni a cikin jihar, musamman ga ma’aikatan gwamnati da sauran waɗanda suka cancanta.

Ya ce shirin na daga cikin Ajandar Gwamna Umar Namadi 12, wadda ta ƙunshi babbar dabarar bunkasa gidaje da raya birane, domin samar da matsuguni mai kyau, rage gibin gidaje, da inganta rayuwar al’umma.

Wannan na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin na faɗaɗa damar samun gidaje masu araha da kuma kyautata jin daɗin jama’a.

Ya kuma bayyana cewa majalisar ta amince da kashe sama da Naira miliyan 914 domin ƙarin ayyuka a kan aikin gina hanyar Chuwasu zuwa Chakwaikwaiwa zuwa Zango Maje, wadda za ta haɗa da hanyar Yan Dutse zuwa Chori.

Sagir ya ce ƙarin ayyukan sun zama wajibi bayan ƙarin binciken fasaha da bitar aikin da aka gudanar, domin ƙara inganta ƙarfinsa da tsarin magudanan ruwa.

Ya ce majalisar ta ce sauyin da aka yi a cikin tsarin aikin zai tabbatar da cewa aikin ya cika ƙa’idojin da ake buƙata, tare da biyan buƙatun zirga-zirgar al’ummomin da za su amfana da shi.

Kwamishinan ya ƙara da cewa, da wannan amincewar, jimillar kuɗin kwangilar aikin ta kai sama da Naira Biliyan 5.4. Yana mai cewa hanyar Chuwasu zuwa Chakwaikwaiwa zuwa Zango Maje muhimmiyar hanya ce ta karkara wadda aka tsara domin inganta haɗin kai tsakanin al’umma, sauƙaƙa jigilar amfanin gona,  ƙara samun damar isa kasuwanni, makarantu da cibiyoyin kiwon lafiya, tare da bunƙasa tattalin arziƙi a yankin da abin ya shafa.

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci6 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara