Labarai
Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda 96 daga gwamnatin tarayya.
Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Jihar da aka gudanar a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
A cewarsa, majalisar ta amince da sayen gidajen ne daga Ma’aikatar Gidaje da Raya Birane ta Tarayya.
Ya bayyana cewa sayen gidajen na da nufin magance matsalar matsuguni a cikin jihar, musamman ga ma’aikatan gwamnati da sauran waɗanda suka cancanta.
Ya ce shirin na daga cikin Ajandar Gwamna Umar Namadi 12, wadda ta ƙunshi babbar dabarar bunkasa gidaje da raya birane, domin samar da matsuguni mai kyau, rage gibin gidaje, da inganta rayuwar al’umma.
Wannan na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin na faɗaɗa damar samun gidaje masu araha da kuma kyautata jin daɗin jama’a.
Ya kuma bayyana cewa majalisar ta amince da kashe sama da Naira miliyan 914 domin ƙarin ayyuka a kan aikin gina hanyar Chuwasu zuwa Chakwaikwaiwa zuwa Zango Maje, wadda za ta haɗa da hanyar Yan Dutse zuwa Chori.
Sagir ya ce ƙarin ayyukan sun zama wajibi bayan ƙarin binciken fasaha da bitar aikin da aka gudanar, domin ƙara inganta ƙarfinsa da tsarin magudanan ruwa.
Ya ce majalisar ta ce sauyin da aka yi a cikin tsarin aikin zai tabbatar da cewa aikin ya cika ƙa’idojin da ake buƙata, tare da biyan buƙatun zirga-zirgar al’ummomin da za su amfana da shi.
Kwamishinan ya ƙara da cewa, da wannan amincewar, jimillar kuɗin kwangilar aikin ta kai sama da Naira Biliyan 5.4. Yana mai cewa hanyar Chuwasu zuwa Chakwaikwaiwa zuwa Zango Maje muhimmiyar hanya ce ta karkara wadda aka tsara domin inganta haɗin kai tsakanin al’umma, sauƙaƙa jigilar amfanin gona, ƙara samun damar isa kasuwanni, makarantu da cibiyoyin kiwon lafiya, tare da bunƙasa tattalin arziƙi a yankin da abin ya shafa.
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai6 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
