Labarai
Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke kara dakile karfin ruwan tare da toshe hanyoyin da yake kwarara.
Hukumar Kula da Kogin Benuwe (UBRBDA) ta bayyana a wata sanarwa cewa matsalar na ƙara tsananta, musamman ga al’ummomin da ke amfana da ruwan kogin, ciki har da aikin noman rani da Geriyo, wanda aka dogaro da shi domin ayyukan ban ruwa.

Binciken da aka gudanar a ranar 2 ga watan Maris na shekarar 2026, da misalin ƙarfe 5 na yamma, ya nuna cewa matakin ruwa ya kai mita 1 da digo 43, yayin da yawan ruwan da ke kwarara ya kai ma’aunin mita 64 a sakan guda, adadin da aka bayyana a matsayin mafi ƙaranci da aka samu a lokacin rani.
Masana sun yi gargadin cewa idan kwararar ruwa na raguwa matuka, taruwar laka kan ƙara tsananta matsalar, lamarin da ke haddasa raguwar zurfin ruwa, toshe hanyoyin shigar ruwa, rage ƙarfin gudun gudun ruwan, da kuma barazana ga wadatar shi domin ban ruwa.

Hukumar ta yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki matakin gaggawa ba, matsalar na iya ƙara muni, tare da shafar wadatar ruwa da ayyukan noma a lokacin rani.
Domin shawo kan matsalar, an fara aikin zurfafa hanyoyin ruwan na musamman, ƙarƙashin kulawar Shugaban Hukumar kuma Babban Jami’in Gudanarwa, Dakta Mahmud Sanusi Mohammed.

A cewar hukumar, aikin zai fi mayar da hankali ne a wuraren da laka ta fi taruwa domin dawo da kwararar ruwa yadda ya kamata, da sauƙaƙa zirga-zirgar ruwa, da kuma samar da ruwa domin ban ruwa ba tare da haddasa wata matsalar ba.
Jami’ai sun bayyana cewa wannan mataki ne na kariya da aka ɗauka bisa sahihan bayanai na kimiyya, maimakon a jira matsalar ta tsananta kafin ɗaukar mataki.
Daga:Yusuf/Safiyah
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
