Connect with us

Labarai

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Published

on

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke kara dakile karfin ruwan tare da toshe hanyoyin da yake kwarara.

Hukumar Kula da Kogin Benuwe (UBRBDA) ta bayyana a wata sanarwa cewa matsalar na ƙara tsananta, musamman ga al’ummomin da ke amfana da ruwan kogin,  ciki har da aikin noman rani da Geriyo, wanda aka dogaro da shi domin ayyukan ban ruwa.

Binciken da aka gudanar a ranar 2 ga watan Maris na shekarar 2026, da misalin ƙarfe 5 na yamma, ya nuna cewa matakin ruwa ya kai mita 1 da digo 43, yayin da yawan ruwan da ke kwarara ya kai  ma’aunin mita 64 a sakan guda, adadin da aka bayyana a matsayin mafi ƙaranci da aka samu a lokacin rani.

Masana sun yi gargadin cewa idan kwararar ruwa na raguwa matuka, taruwar laka kan ƙara tsananta matsalar, lamarin da ke haddasa raguwar zurfin ruwa, toshe hanyoyin shigar ruwa, rage ƙarfin gudun gudun ruwan, da kuma barazana ga wadatar shi domin ban ruwa.

Hukumar ta yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki matakin gaggawa ba, matsalar na iya ƙara muni, tare da shafar wadatar ruwa da ayyukan noma a lokacin rani.

Domin shawo kan matsalar, an fara aikin zurfafa hanyoyin ruwan na musamman,  ƙarƙashin kulawar Shugaban Hukumar kuma Babban Jami’in Gudanarwa, Dakta Mahmud Sanusi Mohammed.

A cewar hukumar, aikin zai fi mayar da hankali ne a wuraren da laka ta fi taruwa domin dawo da kwararar ruwa yadda ya kamata, da sauƙaƙa zirga-zirgar ruwa, da kuma samar da ruwa domin ban ruwa ba tare da haddasa wata matsalar ba.

Jami’ai sun bayyana cewa wannan mataki ne na kariya da aka ɗauka bisa sahihan bayanai na kimiyya, maimakon a jira matsalar ta tsananta kafin ɗaukar mataki.

 Daga:Yusuf/Safiyah

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara