Fasaha
Majalisar Jihar Kano ta Bukaci Gwamnati ta Kafa Cibiyoyin ICT
Daga Khadijah Aliyu
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar da ta kafa cibiyoyin jarabawa da ake amfani da na’urar kwamfuta (CBT) a dukkan kananan hukumomi 44 na jihar, domin dacewa da sabon tsarin jarabawar kammala sakandare WAEC da NECO.
An cimma wannan matsaya ne bayan tattaunawa a zaman majalisar wanda Kakakin Majalisar, Jibril Falgore, ya jagoranta.
Wannan kudiri ya fito ne daga dan majalisa mai wakiltar mazabar Madobi kuma Shugaban Kwamitin Ilimi na Majalisar, Mukhtar Ishaq.
Ya bayyana cewa sabon tsarin ya wajabta gudanar da jarabawa ta hanyar kwamfuta, yana mai jaddada bukatar gaggauta bai wa dalibai kwarewar amfani da na’urar ta kwamfuta.
A cewarsa, kafa cibiyoyin kwamfuta (ICT) a fadin jihar zai taimaka wajen rage gibin fasahar zamani tare da shiryawa dalibai a birane da karkara domin fuskantar jarabawar ta CBT.
Dan majalisa mai wakiltar mazabar Shanono/Bagwai, Ali Lawan, ya goyi bayan kudirin, yana mai cewa lokaci ya yi kuma abu ne mai matukar muhimmanci.
A wani labarin kuma, Majalisar ta bukaci gwamnatin jihar da ta kammala ayyukan samar da wutar lantarki a garuruwan Garun Madadi da Yarguruza da ke karamar hukumar Gwarzo.
Wannan kudiri ya fito ne daga Yunusa Haruna, wanda ya jaddada cewa an riga an zuba kudade masu yawa a aikin, kuma kammala shi zai taimaka wajen magance matsalolin wutar lantarki da ake fama da su.
Da yake goyon bayan kudirin, Sule Lawan Shuwaki mai wakiltar Tudun Wada ya ce kammala aikin zai bunkasa harkokin tattalin arziki a yankin.
Haka kuma, Majalisar ta karbi rahoto kan kudaden Majalisar Masarautar Rano na shekarun 2023–2024, sannan ta amince da kudirori kan gyaran Dam din Buda a Garko da kuma gina hanya a Makoda.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
