Connect with us

Fasaha

Majalisar Jihar Kano ta Bukaci Gwamnati ta Kafa Cibiyoyin ICT

Published

on

Daga Khadijah Aliyu

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar da ta kafa cibiyoyin jarabawa da ake amfani da na’urar kwamfuta (CBT) a dukkan kananan hukumomi 44 na jihar, domin dacewa da sabon tsarin jarabawar kammala sakandare WAEC da NECO.

An cimma wannan matsaya ne bayan tattaunawa a zaman majalisar wanda Kakakin Majalisar, Jibril Falgore, ya jagoranta.

Wannan kudiri ya fito ne daga dan majalisa mai wakiltar mazabar Madobi kuma Shugaban Kwamitin Ilimi na Majalisar, Mukhtar Ishaq.

Ya bayyana cewa sabon tsarin  ya wajabta gudanar da jarabawa ta hanyar kwamfuta, yana mai jaddada bukatar gaggauta bai wa dalibai kwarewar amfani da na’urar ta kwamfuta.

A cewarsa, kafa cibiyoyin kwamfuta (ICT) a fadin jihar zai taimaka wajen rage gibin fasahar zamani tare da shiryawa dalibai a birane da karkara domin fuskantar jarabawar ta CBT.

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Shanono/Bagwai, Ali Lawan, ya goyi bayan kudirin, yana mai cewa lokaci ya yi kuma abu ne mai matukar muhimmanci.

A wani labarin kuma, Majalisar ta bukaci gwamnatin jihar da ta kammala ayyukan samar da wutar lantarki a garuruwan Garun Madadi da Yarguruza da ke karamar hukumar Gwarzo.

Wannan kudiri ya fito ne daga Yunusa Haruna, wanda ya jaddada cewa an riga an zuba kudade masu yawa a aikin, kuma kammala shi zai taimaka wajen magance matsalolin wutar lantarki da ake fama da su.

Da yake goyon bayan kudirin, Sule Lawan Shuwaki mai wakiltar Tudun Wada ya ce kammala aikin zai bunkasa harkokin tattalin arziki a yankin.

Haka kuma, Majalisar ta karbi rahoto kan kudaden Majalisar Masarautar Rano na shekarun 2023–2024, sannan ta amince da kudirori kan gyaran Dam din Buda a Garko da kuma gina hanya a Makoda.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara