Ilimi
Ilimi Shi ne Ginshikin Cigaban Al’umma- Gwamna Namadi
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya jaddada ilimi a matsayin ginshikin ci gaban jihar da makomarta.
Ya bayyana haka ne a bikin yaye dalibai karo na biyu na Jami’ar Sule Lamido da ke Kafin Hausa, inda aka yaye dalibai daga zangon karatu na shekarar 2018/2019 zuwa 2024/2025.
Gwamnan ya ce babu wani fanni da ya fi ilimi muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya da cigaba mai dorewa.Ya taya daliban da suka kammala karatu murna tare da yabawa kokarin shugabannin jami’ar da suka taka rawa wajen ci gabanta tun bayan kafuwarta.

Namadi ya bayyana cewa gwamnatinsa na bai wa ilimi muhimmanci sosai, inda take ware tsakanin kashi 26 zuwa 30 cikin dari na kasafin kudin jihar ga bangaren ilimi, lamarin da ya taimaka wajen inganta gine-gine, koyo da koyarwa, da kuma kara yawan masu shiga makaranta tare da rage yara marasa zuwa makaranta.
Ya kuma ce an mayar da wasu manyan makarantun sakandare cibiyoyin kwarewa domin bunkasa ilimin sana’o’i, tare da kokarin da ake yi na daidaita Kwalejin Babura da tsarin TVET na kasa, domin karfafa ilimin fasaha.

A bangaren ilimin gaba da sakandare, gwamnan ya bayyana cewa jihar ta karbe wata jami’a mai zaman kanta a Majia da ke karamar hukumar Taura, inda ake shirin mayar da ita jami’a ta musamman kan fannin kiwon lafiya da sauran fannoni masu alaka.
Ya ce an riga an kammala matakan tantancewa, yayin da kudirin dokar tabbatar da wannan sauyi ke gaban majalisar dokokin jihar domin amincewa.
Gwamnan ya kuma lissafo wasu manyan ayyuka da ake yi a Jami’ar Sule Lamido, ciki har da gina Kwalejin Kiwon Lafiya, dakunan kwanan dalibai da gidajen ma’aikata.

Sauran ayyukan sun hada da gina gidajen malamai, cibiyar binciken harkar noma da kuma sabon filin taron yaye dalibai.
Jimillar dalibai 4,109 ne aka ba shaidar digirin farko a bikin, wanda ya nuna yadda jami’ar ke ci gaba da habaka a fannin ilimi a cikin shekaru kalilan.
Haka kuma, an nada Sarkin Katagum, Alhaji Umar Faruk na II, a matsayin Uban Jami’ar na biyu, tare da bai wa wasu fitattun mutane uku digirin girmamawa a yayin bikin.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
