Connect with us

Ilimi

Ilimi Shi ne Ginshikin Cigaban Al’umma- Gwamna Namadi

Published

on

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya jaddada ilimi a matsayin ginshikin ci gaban jihar da makomarta.

Ya bayyana haka ne a bikin yaye dalibai karo na biyu na  Jami’ar Sule Lamido da ke Kafin Hausa, inda aka yaye dalibai daga zangon karatu na shekarar  2018/2019 zuwa 2024/2025.

Gwamnan ya ce babu wani fanni da ya fi ilimi muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya da cigaba mai dorewa.Ya taya daliban da suka kammala karatu murna tare da yabawa kokarin shugabannin jami’ar da suka taka rawa wajen ci gabanta tun bayan kafuwarta.

Namadi ya bayyana cewa gwamnatinsa na bai wa ilimi muhimmanci sosai, inda take ware tsakanin kashi 26 zuwa 30 cikin dari na kasafin kudin jihar ga bangaren ilimi, lamarin da ya taimaka wajen inganta gine-gine, koyo da koyarwa, da kuma kara yawan masu shiga makaranta tare da rage yara marasa zuwa makaranta.

Ya kuma ce an mayar da wasu manyan makarantun sakandare cibiyoyin kwarewa domin bunkasa ilimin sana’o’i, tare da kokarin da ake yi na daidaita Kwalejin Babura da tsarin TVET na kasa, domin karfafa ilimin fasaha.

A bangaren ilimin gaba da sakandare, gwamnan ya bayyana cewa jihar ta karbe wata jami’a mai zaman kanta a Majia da ke karamar hukumar Taura, inda ake shirin mayar da ita jami’a ta musamman kan fannin kiwon lafiya da sauran fannoni masu alaka.

Ya ce an riga an kammala matakan tantancewa, yayin da kudirin dokar tabbatar da wannan sauyi ke gaban majalisar dokokin jihar domin amincewa.

Gwamnan ya kuma lissafo wasu manyan ayyuka da ake yi a Jami’ar Sule Lamido, ciki har da gina Kwalejin Kiwon Lafiya, dakunan kwanan dalibai da gidajen ma’aikata.

Sauran ayyukan sun hada da gina gidajen malamai, cibiyar binciken harkar noma da kuma sabon filin taron yaye dalibai.

Jimillar dalibai 4,109 ne aka ba shaidar digirin farko a bikin, wanda ya nuna yadda jami’ar ke ci gaba da habaka a fannin ilimi a cikin shekaru kalilan.

Haka kuma, an nada Sarkin Katagum, Alhaji Umar Faruk na II, a matsayin Uban Jami’ar na biyu, tare da bai wa wasu fitattun mutane uku digirin girmamawa a yayin bikin.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara