Connect with us

Fasaha

An sami Ci gaba a bangaren Sufuri – Farfesa Umar

Published

on

Shugaban Jami’ar Sufuri ta Gwamnatin Tarayya dake Daura Jahar Katsina Farfesa Umar Adam Katsayal ya bayyana haka yayin zantawarshi da Radio Nigeria Kaduna.

A cewar Farfesa Umar Adam Katsayal kafin samun ‘Yan cin kai hanyoyin Mota hanya daya ne ba tagwayen hanyoyi ba sai bayan samun ‘yan cin kai aka fara samar da tagwayen hanyoyi tare ma da samun hanyoyin Mota da Suka hada garuruwa baya ga samun hanyoyin gadojin Mota na sama a manyan garuruwa da biranen kasa, hakama ta bangaren Filayen Jiragen Sama.

Shugaban Jami’ar Sufurin ya bayyana cewa kafin samun ‘yan cin kai sai a Birnin Ikko da Kano ake da tashoshin sauka da tashin Jiragen Sama da a yanzu kusan Jahohin wannan kasa ke da tashoshin sauka da tashin Jiragen Sama dama kokarin Samar da tashoshin Jiragen sama na dakon kaya.

Da ya juwa ta bangaren Sufurin tashoshin ruwa ya bayyana yadda ake dakon kaya daga wasu kasashe zuwa Nijeriya a tashoshin ruwa tare ma da samar da hanyoyin Jiragen kasa fiye da wadanda turawan mulkin mallaka suka bari da yanzu ma ake kokarin hada titin Jirgin kasa zuwa Jamhuriyar Niger baya ga tashoshin kan tudu da ake dako da sauke kaya.

Farfesa Umar Adam Katsayal ya bayyana ci gaba da aka samu a fannin Sufuri ta hanyar samar da Jami’ar Sufurin ta Gwamnatin Tarayya dake Daura domin inganta harkokin Sufuri a Nigeria da wannan Jami’a ita ce Jami’a irin ta ta farko a Nahiyar Africa.

A karshe Shugaban Jami’ar Sufurin ta Gwamnatin Tarayya dake Daura Farfesa Umar Adam Katsayal ya taya Shugaban kasa Bola Tinubu murnar cikar Nigeria Shekaru 65 da samun ‘yan cin kai da Mataimakinshi hadi da Shugabannin Majalisun Tarayyar Nigeria da Ministocin Sufuri da Ilmi a Tarayya Nigeria dama daukacin al’ummar Nigeria tare da kira ga ‘yan Kasa na ci gaba da yiwa Nigeria addu’o’in samun ci gaba da habakar tattalin arziki dama samun tsaro da zaman lafiya.

Ibrahim Idris Kaura Namoda/Kaduna

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara