Connect with us

Labarai

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Published

on

Daga Ali Muhammad Rabi’u 

Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta shigowa da su ko kuma aka takaita, da kudinsu ya haura Naira miliyan 478 a bana.

Mukaddashin shugaban hukumar  a yankin Jihar Kwara, Mataimakin Kwanturola Najeem Ogundeyi ne ya bayyana hakan yayin zantawarsa da manema labarai kan ayyukan hukumar a jihae .

Ya ce hukumar ta kuma samar wa gwamnati kudaden shiga da suka kai sama da Naira biliyan 2 da miliyan 500, wanda hakan ke nuna irin gudunmawar da take bayarwa wajen tallafawa manufofin tattalin arzikin gwamnati.

A cewarsa, hukumar na da kudurin kare tattalin arzikin kasa tare da tabbatar da bin doka da oda.

Ogundeyi ya kara da cewa hukumar za ta tabbatar da cewa jihar ba ta zama mafakar masu safarar haramtattun kayayyaki ba, yana mai gargadin cewa duk wanda ya yi yunkurin tauye tattalin arzikin kasa ta hanyar fasa kwauri zai fuskanci hukunci mai tsauri.

Ya bayyana cewa duk da gargadi da ake yi akai-akai, har yanzu ana ci gaba da safarar kaya ta barauniyar hanya, musamman shigo da shinkafa daga kasashen waje ba bisa ka’ida ba, lamarin da ke barazana ga manoman gida da kuma samar da abinci a kasa.

Ogundeyi ya ce haramta shigo da irin wannan shinkafa wata muhimmiyar dabara ce ta karfafa gwiwar manoma na cikin gida, samar da ayyukan yi, da kuma wadata kasa da abinci.

Ya kara jaddada cewa wadannan nasarorin da aka samu sun samo asali ne daga sahihan bayanan sirri da kuma hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro.

Ya kuma yi kira ga mazauna yankunan kan iyaka, ‘yan kasuwa da daukacin jama’a da su hada kai da hukumar domin kare masana’antun cikin gida, kiyaye tattalin arzikin kasa, da kuma bunkasa ci gaba mai dorewa.

Daga cikin kayayyakin da rundunar ta kama sun hada da motoci guda biyar, buhuna 1,107 na shinkafar  waje, buhuna 44 na sukari da aka shigo da su daga kasashen waje, jarkoki 317 na man fetur (PMS), buhuna 120 na ma’adinin lithium da aka hako ba bisa ka’ida ba, da kuma daruruwan kayan sawa wato gwanjo,  da kayayyakin gyaran motoci.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara