Labarai
Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi
Daga Bello Wakili
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin Minista a Ma’aikatar.
An gudanar da bikin rantsarwar a Fadar Shugaban Ƙas, inda Shugaba Tinubu ya taya sabon ministan murna, tare da bayyana kwarin gwiwarsa kan cewa zai taimaka wajen aiwatar da manufofin gyaran tattalin kasa.
Shugaban ƙasar ya yaba wa Oyedele kan rawar da ya taka wajen jagorantar kokarin gyara tsarin haraji na Najeriya, inda ya bayyana cewa tsohon tsarin harajin ƙasar ya tsufa kuma yana bukatar sabuntawa domin ya taimaka wajen bunƙasa tattalin arziki da kuma tabbatar da gaskiya da rikon amana.

A nasa jawabin, sabon Ministan ya gode wa Shugaban ƙasa bisa amincewar da ya nuna masa, yana mai cewa damar da aka ba shi ta yi wa ƙasa hidima babbar abar alfahari ce.
Ya kuma tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa zai ba da dukkan ƙoƙarinsa wajen gudanar da aikinsa, yana mai cewa manufofin kudin gwamnati za su mayar da hankali kan ƙarfafa tattara kudaden shiga, inganta yadda ake kashe kuɗi, da kuma tabbatar da dorewar tattalin arzikin ƙasa.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
