Connect with us

Labarai

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Published

on

Daga Sani Dutsinma

Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah daga Gidauniyar NASARA a Jihar Kebbi.

Babbar Sakatariyar Yaɗa Labarai ta Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Khadijat Saidu ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta rabawa manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

Sanarwar ta ce an bada tallafin ne domin sanya farin ciki a zukatan marayu da zawarawa 1,000 a garin Kangiwa, a watan Ramadan da kuma bukukuwan Sallah.

Ta ƙara da cewa, Gidauniyar NASARA wadda Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris ta kafa, ta raba kayan Sallah ga marayu, yayin da aka bai wa zawarawa buhunan shinkafa domin su sami damar yin bukin Sallah cikin farin ciki tare da iyalansu.

Tawagar gidauniyar ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abdulrasheed Bala, wanda shi ne jami’in da ke kula da Gidauniyar a matakin jiha, ta isar da saƙon Uwargidan Gwamnan, inda ta jaddada muhimmancin kyautatawa da nuna karamci, musamman a wannan lokaci na watan Ramadan.

A cewarsa, wannan kyakkyawan shiri na daga cikin ƙoƙarin Hajiya Zainab na tabbatar da cewa kowa yana cikin annashuwa a wannan lokaci na ibada. Ya ƙara da cewa ayyukan alherin da gidauniyar ke yi suna da matuƙar tasiri a rayuwar marasa galihu.

Wasu daga cikin waɗanda suka amfana da tallafin sun bayyana farin cikinsu tare da gode wa Allah Madaukakin Sarki, sannan suka nuna matuƙar godiya ga wadda ta kafa gidauniyar, Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris, da kuma tawagar Gidauniyar NASARA bisa wannan karamci da kulawa da suka nuna.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara