Labarai
Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu
Daga Sani Dutsinma
Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah daga Gidauniyar NASARA a Jihar Kebbi.
Babbar Sakatariyar Yaɗa Labarai ta Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Khadijat Saidu ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta rabawa manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

Sanarwar ta ce an bada tallafin ne domin sanya farin ciki a zukatan marayu da zawarawa 1,000 a garin Kangiwa, a watan Ramadan da kuma bukukuwan Sallah.
Ta ƙara da cewa, Gidauniyar NASARA wadda Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris ta kafa, ta raba kayan Sallah ga marayu, yayin da aka bai wa zawarawa buhunan shinkafa domin su sami damar yin bukin Sallah cikin farin ciki tare da iyalansu.

Tawagar gidauniyar ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abdulrasheed Bala, wanda shi ne jami’in da ke kula da Gidauniyar a matakin jiha, ta isar da saƙon Uwargidan Gwamnan, inda ta jaddada muhimmancin kyautatawa da nuna karamci, musamman a wannan lokaci na watan Ramadan.
A cewarsa, wannan kyakkyawan shiri na daga cikin ƙoƙarin Hajiya Zainab na tabbatar da cewa kowa yana cikin annashuwa a wannan lokaci na ibada. Ya ƙara da cewa ayyukan alherin da gidauniyar ke yi suna da matuƙar tasiri a rayuwar marasa galihu.

Wasu daga cikin waɗanda suka amfana da tallafin sun bayyana farin cikinsu tare da gode wa Allah Madaukakin Sarki, sannan suka nuna matuƙar godiya ga wadda ta kafa gidauniyar, Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris, da kuma tawagar Gidauniyar NASARA bisa wannan karamci da kulawa da suka nuna.

-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
