Connect with us

Labarai

Majalisar Dokokin Kaduna Ta Amince da Sabbin Dokoki kan Sauyin Yanayi da Haraji

Published

on

Daga Shamsuddeen Mannir Atiku

Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da wasu muhimman dokoki guda biyu da suka shafi sauyin yanayi da kuma tsarin haraji, domin inganta rayuwar al’umma da bunkasa tattalin arzikin jihar.

A bangaren sauyin yanayi, majalisar ta amince da kudirin doka na kafa Hukumar Ba da Shawara kan Sauyin Yanayi ta Jihar Kaduna, wadda za ta rika bai wa gwamnati shawarwari kan hanyoyin yaki da sauyin yanayi, kare muhalli, da kuma fuskantar kalubalen da ke tattare da sauyin yanayi.

Shugaban Majalisar, Yusuf Dahiru Liman, ya bayyana cewa sabuwar hukumar za ta taimaka wajen tsara matakan da za su rage illolin sauyin yanayi kamar ambaliya, fari, da kwararowar hamada, tare da jaddada muhimmancin hadin kan al’umma wajen kare muhalli domin inganta lafiya da rayuwa.

Da yake gabatar da rahoton kwamitin, Shugaban Kwamitin Muhalli da Albarkatun Kasa, Usman Danlami Stingo, ya ce hukumar za ta kuma taimaka wa jihar wajen samun tallafi daga kungiyoyi da hukumomin kasa da kasa, tare da kula da dukkan batutuwan da suka shafi muhalli. Ya kara da cewa mambobin hukumar za su hada da wakilai daga hukumomin gwamnati, kungiyoyin farar hula, kungiyoyin addini da sauran masu ruwa da tsaki.

Usman Danlami Stingo, Shugaban Kwamitin Muhalli da Albarkarun Kasa na Majalisar Dokokin Jihar Kaduna

A wani bangare kuma, majalisar ta soke Dokar Tattarawa da Tsara Haraji ta shekarar 2020, tare da kafa sabuwar Dokar Harajin Jihar Kaduna ta shekarar 2025.

Shugaban Majalisar ya ce sabuwar dokar ta tattara dukkan tanade-tanaden haraji cikin tsari guda domin saukaka fahimta da aiwatarwa, tare da kawar da maimaituwa da tsofaffin dokoki da suka daina dacewa da zamani.

Tun da farko, Shugaban Kwamitin Harkokin Kudi, Halliru Bello Dangana, ya bayyana cewa bayan nazari mai zurfi, kwamitin ya ga dacewar samar da sabuwar dokar da za ta hada dukkan nau’o’in haraji cikin kundin doka guda daya da aka sabunta.

Halliru Bello Dangana, Shugaban Kwamitin Kudi na Majalisar Dokokin Jihar Kaduna

Ya kara da cewa sabuwar dokar za ta taimaka wajen toshe hanyoyin asarar kudaden haraji da kuma kara yawan kudaden shiga na jihar, wanda hakan zai tallafa wa ayyukan ci gaba da gina ababen more rayuwa.

 

Majalisar ta jaddada cewa wadannan dokoki biyu za su taka muhimmiyar rawa wajen inganta muhalli da kuma karfafa tattalin arzikin Jihar Kaduna.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara