Labarai
Hukumar Alhazai ta Kasa ta Kai Ziyarar Gani-da-Ido Jihar Jigawa
Daga Usman Muhammad Zaria
Hukumar Alhazai ta Ƙasa NAHCON ta kai ziyarar gani da ido a filin jirgin sama da sansanin Alhazai na Jihar Jigawa a cigaba da shirye-shiryen aikin Hajjin shekarar 2026.
Tawagar wadda Kwamishinan NAHCON na shiyyar Arewa maso Yamma, Sheikh Muhammad Bin Uthman ya jagoranta, ta samu tarba daga Daraktan Gudanarwa da Kudi na Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Alhaji Muhammad Umar Sambo, a madadin shugaban hukumar.

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Alhaji Habibu Yusuf Babura ya rabawa manema labarai, ya ce tawagar ta duba wuraren tantance Alhazai a sansanin.
A cewarsa, tawagar ta kuma duba kayayyakin aiki da ke Filin Jirgin Sama na Nuhu Muhammadu Sunusi da ke Dutse, babban birnin jihar.

Sheikh Bin Uthman ya bayyana gamsuwarsa da yadda jihar ta shirya wajen karɓa da tantance dukkan Maniyyata kafin tashinsu zuwa ƙasa mai tsarki.
Ya yabawa Gwamnatin Jihar Jigawa bisa ci gaba da goyon baya da jajircewa wajen kula da jin daɗin Alhazai, musamman wajen samar da masauki, kula da lafiya da sauran harkokin tafiyarsu zuwa mai tsarki.

A shekarar 2025, an yaba wa Jihar Jigawa bisa kyakkyawan tsari da gudanar da aikin Hajji, inda tawagar NAHCON ta nuna kyakkyawan fata cewa jihar za ta ci gaba da riƙe wannan kambu a shekarar 2026.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
