Connect with us

Labarai

Hukumar Alhazai ta Kasa ta Kai Ziyarar Gani-da-Ido Jihar Jigawa

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Alhazai ta Ƙasa NAHCON ta kai ziyarar gani da ido a filin jirgin sama da sansanin Alhazai na Jihar Jigawa a cigaba da shirye-shiryen aikin Hajjin shekarar 2026.

Tawagar wadda Kwamishinan NAHCON na shiyyar Arewa maso Yamma, Sheikh Muhammad Bin Uthman ya jagoranta, ta samu tarba daga Daraktan Gudanarwa da Kudi na Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Alhaji Muhammad Umar Sambo, a madadin shugaban hukumar.

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Alhaji Habibu Yusuf Babura ya rabawa manema labarai, ya ce tawagar ta duba wuraren tantance Alhazai a sansanin.

A cewarsa, tawagar ta kuma duba kayayyakin aiki da ke Filin Jirgin Sama na Nuhu Muhammadu Sunusi da ke Dutse, babban birnin jihar.

Sheikh Bin Uthman ya bayyana gamsuwarsa da yadda jihar ta shirya wajen karɓa da tantance dukkan Maniyyata kafin tashinsu zuwa ƙasa mai tsarki.

Ya yabawa Gwamnatin Jihar Jigawa bisa ci gaba da goyon baya da jajircewa wajen kula da jin daɗin Alhazai, musamman wajen samar da masauki, kula da lafiya da sauran harkokin tafiyarsu  zuwa mai tsarki.

A shekarar 2025, an yaba wa Jihar Jigawa bisa kyakkyawan tsari da gudanar da aikin Hajji, inda tawagar NAHCON ta nuna kyakkyawan fata cewa jihar za ta ci gaba da riƙe wannan kambu a shekarar 2026.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara