Labarai
Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa
Daga Bello Wakili
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN, wanda ake sa ran Majalisar Dattijai za ta tabbatar da shi.
Nominaciyar tana bisa tanadin Sashe na 8, sakin layi na 1 na Dokar Central Bank of Nigeria Act 2007.
Nadin Yuguda ya biyo bayan nadin tsohon Mataimakin Gwamnan, Bala Bello, a matsayin Mashawarci na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Tattalin Arziki.
Shugaba Tinubu ya bukaci Yuguda da sauran jami’an bankin da su gudanar da ayyukansu bisa jajircewa, ƙwarewa, da sadaukarwa, domin tabbatar da daidaiton tattalin arziki da ci gaban kasa.
Lamido Yuguda ya taba rike mukamin slShugaban Hukumar Kasuwannin Hannun Jari daga shekarar 2020 zuwa 2024.
Ya samu digiri na farko a fannin Lissafi na Kasuwanci (Accountancy) aa Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya a shekarar 1983, sannan daga baya ya samu digiri na biyu a fannin Kudi, wato Banking and Finance daga Jami’ar Birmingham a shekarar 1991.
Yuguda memba ne a Cibiyar Ƙwararrun Masu Lissafi ta Najeriya (ICAN) kuma Ƙwararren Masanin Kudi.
Ya fara aikinsa a CBN a shekarar 1984 a matsayin Babban Mai Kula da Ayyuka a Sashen Harkokin Kudi na kasashen Waje.
Daga baya ya yi aiki a matsayin masanin tattalin arziki a sashen Afrika a Asusun Bada Lamuni na Duniya daga shekarar 1997 zuwa 2001 kafin ya koma CBN.
Ya yi ritaya daga CBN a shekarar 2016 bayan ya shugabanci Sashen Gudanar da Ajiyar Kudi na tsawon shekaru shida.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
