Connect with us

Labarai

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Published

on

Daga Bello Wakili

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN, wanda ake sa ran Majalisar Dattijai za ta tabbatar da shi.

Nominaciyar tana bisa tanadin Sashe na 8, sakin layi na 1 na Dokar Central Bank of Nigeria Act 2007.

Nadin Yuguda ya biyo bayan nadin tsohon Mataimakin Gwamnan, Bala Bello, a matsayin Mashawarci na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Tattalin Arziki.

Shugaba Tinubu ya bukaci Yuguda da sauran jami’an bankin da su gudanar da ayyukansu bisa jajircewa, ƙwarewa, da sadaukarwa, domin tabbatar da daidaiton tattalin arziki da ci gaban kasa.

Lamido Yuguda ya taba rike mukamin slShugaban Hukumar Kasuwannin Hannun Jari daga shekarar 2020 zuwa 2024.

Ya samu digiri na farko a fannin Lissafi na Kasuwanci (Accountancy) aa Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya  a shekarar 1983, sannan daga baya ya samu digiri na biyu a fannin Kudi, wato Banking and Finance daga Jami’ar Birmingham a shekarar 1991.

Yuguda memba ne a Cibiyar Ƙwararrun Masu Lissafi ta Najeriya (ICAN)  kuma Ƙwararren Masanin Kudi.

Ya fara aikinsa a CBN a shekarar 1984 a matsayin Babban Mai Kula da Ayyuka a Sashen Harkokin Kudi na kasashen Waje.

Daga baya ya yi aiki a matsayin masanin tattalin arziki a sashen Afrika a Asusun Bada Lamuni na Duniya daga shekarar 1997 zuwa 2001 kafin ya koma CBN.

Ya yi ritaya daga CBN a shekarar 2016 bayan ya shugabanci Sashen Gudanar da Ajiyar Kudi na tsawon shekaru shida.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara