Connect with us

Kasuwanci

‘Yan Kasuwar Albasa a Najeriya Sun Dakatar da Fitar da Kaya Zuwa Ghana

Published

on

Daga Nasir Malali 

’Yan Kasuwar Albasa a Najeriya sun dakatar da fitar da albasa zuwa Jamhuriyar Ghana sakamakon wani sabani da aka samu.

A cikin wata sanarwa ta hadin gwiwa da shugabannin kungiyoyin ’yan kasuwar albasa suka fitar a Sakkwato,  wadda aka rabawa manema labarai, sun ce wannan mataki ya biyo bayan yawaitar hare-hare da ake kai wa ’yan kasuwarsu, musamman a kasuwar Kotoku, wacce take muhimmiyar cibiyar kasuwanci ce a babban birnin Ghana.

A cewar ’yan kasuwar, lamarin ya kara kamari ne bayan wata takaddama tsakanin ’yan kasuwar Najeriya da na Ghana wadda ake zargin ta kai ga kwace manyan motoci dauke da albasa mallakar ’yan kasuwar Najeriya.

Wannan lamari, wanda ke barazana ga wani muhimmin bangare na kasuwancin noma a yankin kasashen Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Afirka ta Yamma ECOWAS, ya janyo damuwa kan tsaron ’yan kasuwar Najeriya da kuma dorewar harkokin kasuwancin kan iyaka tsakanin kasashen biyu.

Sanarwar ta kara da cewa dakatarwar za ta ci gaba da kasancewa har sai an warware dukkan matsalolin da ke akwai tare da dawo da yanayi na kasuwanci mai aminci, adalci da bin doka.

Ta kuma yi kira ga hukumomin da abin ya shafa a Najeriya da Ghana, tare da kungiyoyin yankin, da su gaggauta binciken abubuwan da aka ruwaito, ciki har da kwace motocin albasa na ’yan Najeriya, domin hana sake faruwar irin wannan rikici a nan gaba.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara