Kasuwanci
‘Yan Kasuwar Albasa a Najeriya Sun Dakatar da Fitar da Kaya Zuwa Ghana
Daga Nasir Malali
’Yan Kasuwar Albasa a Najeriya sun dakatar da fitar da albasa zuwa Jamhuriyar Ghana sakamakon wani sabani da aka samu.
A cikin wata sanarwa ta hadin gwiwa da shugabannin kungiyoyin ’yan kasuwar albasa suka fitar a Sakkwato, wadda aka rabawa manema labarai, sun ce wannan mataki ya biyo bayan yawaitar hare-hare da ake kai wa ’yan kasuwarsu, musamman a kasuwar Kotoku, wacce take muhimmiyar cibiyar kasuwanci ce a babban birnin Ghana.
A cewar ’yan kasuwar, lamarin ya kara kamari ne bayan wata takaddama tsakanin ’yan kasuwar Najeriya da na Ghana wadda ake zargin ta kai ga kwace manyan motoci dauke da albasa mallakar ’yan kasuwar Najeriya.
Wannan lamari, wanda ke barazana ga wani muhimmin bangare na kasuwancin noma a yankin kasashen Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Afirka ta Yamma ECOWAS, ya janyo damuwa kan tsaron ’yan kasuwar Najeriya da kuma dorewar harkokin kasuwancin kan iyaka tsakanin kasashen biyu.
Sanarwar ta kara da cewa dakatarwar za ta ci gaba da kasancewa har sai an warware dukkan matsalolin da ke akwai tare da dawo da yanayi na kasuwanci mai aminci, adalci da bin doka.
Ta kuma yi kira ga hukumomin da abin ya shafa a Najeriya da Ghana, tare da kungiyoyin yankin, da su gaggauta binciken abubuwan da aka ruwaito, ciki har da kwace motocin albasa na ’yan Najeriya, domin hana sake faruwar irin wannan rikici a nan gaba.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
