Connect with us

Labarai

Gwamnatin Zamfara ta Jinjinawa Hukumomin Tsaro Bisa Wanzar da Zaman Lafiya a Jihar

Published

on

Daga Aminu Dalhatu

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana jin daɗinta tare da yaba wa hukumomin tsaro da ke aiki a jihar bisa nasarar da suka samu a yaƙi da rashin tsaro, musamman a wani sabon samame da ya kai ga hallaka kimanin ’yan bindiga 100.

Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na jihar, Mahmud Mohammed Dantawasa, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa, inda ya ce wannan nasara hujja ce karara ta  ƙwazo da ƙwarewar jami’an tsaro, waɗanda ke ci gaba da sadaukar da rayukansu domin kare al’umma a sassan jihar.

A cewarsa, gwamnatin jihar na matuƙar yaba wa sadaukarwarsu da jajircewarsu wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Zamfara.

Mahmud Dantawasa ya ƙara da cewa wannan nasara babbar alama ce ta ci gaba a ƙoƙarin da ake yi na rushe ƙungiyomasu’yan ta’adda, da kawar da barazanar ’yan bindiga da ta addabi yankuna da dama na jihar.

Ya jaddada cewa gwamnatin jihar na ƙarfafa gwiwar jami’an tsaro da su ci gaba da zama jajirtattu, da ci gaba da aiki tuƙuru.

Gwamnatin ta kuma tabbatar musu da cikakken goyon baya da kuma ci gaba da ba su tallafin kayan aiki, tare da yin kira agare su da kada su yi ƙasa a gwiwa har sai an tabbatar da tsaro a dukkan sassan jihar.

Haka kuma, gwamnatin jihar ta sake jaddada aniyarta ta ƙarfafa haɗin gwiwa da Gwamnatin Tarayya da dukkan masu ruwa da tsaki a harkar tsaro, tare da alƙawarin ci gaba da bayar da duk wani tallafi da ake buƙata domin nasarar ayyukan tsaro a yanzu da ma nan gaba.

A ƙarshe, kwamishinan ya yi kira ga al’ummar Zamfara da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro haɗin kai ta hanyar ba da bayanai a kan lokaci da kuma kula da tsaro a cikin al’umma.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara