Connect with us

Labarai

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da bayar da tallafin kuɗi ga ma’aikatan gwamnati da na gidan gwamnati su 3,682 a jihar.

Ya bayyana cewa wannan shiri wani ɓangare ne na tsarin kula da jin daɗin ma’aikatan gwamnatinsa, wanda ke da nufin tallafa wa ma’aikata da sauran marasa ƙarfi, musamman a cikin watan Ramadan.

A cewarsa, kayan tallafin da suka haɗa da shinkafa, da taliya da sauran muhimman kayan abinci, an samar da su ne domin bai wa ma’aikata da iyalansu damar gudanar da azumi cikin sauƙi da walwala.

Ya ƙara da cewa wannan tallafi ya zo ne a matsayin kari ga sauran shirye-shiryen tallafin Ramadan da ake aiwatarwa a faɗin jihar.

Hakan ya haɗa da babban shirin ciyarwa da ake gudanarwa a kusan cibiyoyi 640 da ke cikin gundumomin siyasa 287.

Bayan samar da abinci, Gwamna Namadi ya ce shirin na kuma taimakawa tattalin arzikin cikin gida, ta hanyar samar da ayyukan wucin gadi ga kusan mutane 6,000, ciki har da masu girki da masu kula da rabon kayan abinci.

Ya kuma ƙara da cewa gwamnati ta faɗaɗa shirin domin ya haɗa da makarantun Tsangaya, inda makarantu 562 a cikin ƙananan hukumomi 27 ke cin gajiyar shirin a wannan watan Ramadan.

Da yake bayyana watan mai alfarma a matsayin lokaci na tausayi, sadaukarwa da kyautatawa, Gwamnan ya jaddada alhakin gwamnatinsa na ƙarfafa haɗin kai ta hanyar shirye-shiryen jin ƙai da aka tsara yadda ya dace.

Ya kuma ce rabon kayan abinci ga ma’aikata na nuna yadda gwamnatinsa ke girmama gudummawar da suke bayarwa wajen bunƙasa jihar. Yana mai cewa za a bai wa kowane daga cikin wadanda suka amfana da tallafin kuɗi  naira 20,000, inda jimillar kuɗin da za a raba ta haura naira miliyan 12.

Don haka, Malam Umar Namadi ya yi kira ga al’umma da su yi aiki da koyarwar addinin Musulunci ta hanyar taimakon juna tare da yin addu’o’i domin zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba mai ɗorewa a Jihar Jigawa da Najeriya baki ɗaya.

A nasa jawabin, Kwamishinan Ma’aikatar Jin Kai, Alhaji Auwalu Sankara, ya yaba wa gwamnan bisa faɗaɗa shirye-shiryen tallafin Ramadan a jihar.

Ya ce adadin waɗanda ke amfana da shirin ciyarwar Ramadan ya ƙaru sosai a ƙarƙashin wannan gwamnati, inda ya tashi daga kusan mutane miliyan shida zuwa sama da miliyan takwas.

Ya ce ci gaba da faɗaɗa shirin a kowace shekara na nuna ƙudirin gwamnati na tabbatar da cewa babu wanda zai shiga watan Ramadan cikin yunwa.

Ma’aikatar Jin Kai da Agajin Gaggawa ce ke kula da rabon tallafin tare da haɗin gwiwar Ofishin Shugaban Ma’aikatan Jiha domin tabbatar da gaskiya da rikon amana.

Wasu daga cikin waɗanda suka amfana sun nuna godiyarsu ga Gwamna Namadi, inda suka bayyana tallafin a matsayin wanda ya zo a kan lokaci, la’akari da tsadar rayuwa da ake fuskanta a halin yanzu.

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci7 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara