Labarai
Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo
Daga Abdullahi Jalaluddeen
Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki 257 da aka sata a wani aikin tsaro na haɗin gwiwa a Ƙaramar Hukumar Gwarzon Jihar Kano.
An gudanar da aikin ne ta haɗin gwiwar rundunar tsaro karkashin Bataliya ta 3, bayan samun kiran gaggawa daga mazauna yankin.
Mataimakin Daraktan Harkokin Yada Labarai na Soji, Majar Babatunde Zubair, ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Kano.
Ya ce rundunar tsaron ta samu kiran gaggawa ne da misalin ƙarfe 6 na safe ranar 1 ga watan Maris, inda suka garzaya inda lamarin ya faru nan take.
A cewarsa, sojojin sun yi musayar wuta da ‘yan bindigar inda suka samu nasarar dawo da dabbobin da aka sata, waɗanda suka haɗa da Shanu, Awakai da Jaki guda daya.
Manjo Zubair ya ƙara da cewa an mika dabbobin da aka dawo da su ga masu su, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin bin sawu don kamo ‘yan bindigarda suka tsere.
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai6 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
