Connect with us

Fasaha

Shugaba Tinubu Ya Haramta Fitar Da Man Kade daga Nijeriya

Published

on

Shugaban Kasa, Bola Tinubu ya bayar da umarnin dakatar da fitar da ɗanyen man kaɗe daga ƙasar na tsawon watanni shida domin ƙarfafa sarrafa shi a cikin gida da bunƙasa harkar masana’antar man kaɗen wanda kashi 95 na masu sarrafawa mata ne.

Tinubu ya bayyana kaɗe a matsayin ‘arziƙin Najeriya da ke cikin daji’.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima ne ya sanar da matakin a wurin taron masu ruwa da tsaki daga ɓangarori daban-daban a Abuja’ kuma shi ne zai jagoranci kwamiti na musamman da aka kafa domin faɗaɗa shirin sarrafa kaɗe cikin gaggawa

Kashim ya ce wannan ba mataki ne na kawo cikas ga harkokin cinikayya ba, sai dai an ɗauki matakin ne domin samar da daraja ga ƙasar da ƙara samar da ayyukan yi da kuma ƙara kuɗaɗen shiga.

Najeriya na daga cikin ƙasashe mafiya samar da kaɗe a duniya, musamman a jihohin Neja da Kwara da Oyo inda take samar da kusan kashi 40 na ɗanyen man kaɗe a duniya, amma tana da kashi ɗaya ne kacal a kasuwar da darajarta ta kai dala biliyan 6.5.

Gwamnati ta kuma ce ana fitar da kusan tan 90,000 na kaɗe ba bisa ƙa’ida ba a kowace shekara, abin da ke sa masana’antun cikin gida gaza yin aiki yadda ya kamata.

Mataimakin shugaban ƙasar ya ƙara da cewa “Matakin zai iya samar da dala miliyan 300 duk shekara a nan gaba kaɗan tare da nufin nunka hakan nan da shekara ta 2027.

Bello Wakili, Abuja

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci6 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara