Fasaha
Shugaba Tinubu Ya Haramta Fitar Da Man Kade daga Nijeriya
Shugaban Kasa, Bola Tinubu ya bayar da umarnin dakatar da fitar da ɗanyen man kaɗe daga ƙasar na tsawon watanni shida domin ƙarfafa sarrafa shi a cikin gida da bunƙasa harkar masana’antar man kaɗen wanda kashi 95 na masu sarrafawa mata ne.
Tinubu ya bayyana kaɗe a matsayin ‘arziƙin Najeriya da ke cikin daji’.
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima ne ya sanar da matakin a wurin taron masu ruwa da tsaki daga ɓangarori daban-daban a Abuja’ kuma shi ne zai jagoranci kwamiti na musamman da aka kafa domin faɗaɗa shirin sarrafa kaɗe cikin gaggawa
Kashim ya ce wannan ba mataki ne na kawo cikas ga harkokin cinikayya ba, sai dai an ɗauki matakin ne domin samar da daraja ga ƙasar da ƙara samar da ayyukan yi da kuma ƙara kuɗaɗen shiga.
Najeriya na daga cikin ƙasashe mafiya samar da kaɗe a duniya, musamman a jihohin Neja da Kwara da Oyo inda take samar da kusan kashi 40 na ɗanyen man kaɗe a duniya, amma tana da kashi ɗaya ne kacal a kasuwar da darajarta ta kai dala biliyan 6.5.
Gwamnati ta kuma ce ana fitar da kusan tan 90,000 na kaɗe ba bisa ƙa’ida ba a kowace shekara, abin da ke sa masana’antun cikin gida gaza yin aiki yadda ya kamata.
Mataimakin shugaban ƙasar ya ƙara da cewa “Matakin zai iya samar da dala miliyan 300 duk shekara a nan gaba kaɗan tare da nufin nunka hakan nan da shekara ta 2027.
Bello Wakili, Abuja
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai6 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
