Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoma 352 A Nasarawa Da Kayayyakin Noma Na Zamani

Published

on

Gwamnatin Tarayya tare da Asusun Samar da Kudade Domin Bunkasa Harkokin Noma(IFAD) da Shirin Sarrafa Amfanin Gona (VCDP) sun fara raba kayayyakin noman zamani da mashin mai kafa uku  ga manoma 352 a Jihar Nasarawa domin kakar noman bana.

Shugabar shirin IFAD-VCDP, Dr. Eunice Adgidzi ce ta kaddamar da rabon kayayyakin a Lafiya, babban birnin jihar, inda ta ta bayyana cewa shirin ya fi karkata ne ga kanana manoman shinkafa da rogo.

Ta ce shirin wani bangare ne na ƙoƙarin da ake yi na sauya fannin noma zuwa abin da zai kawo wadatar abinci, samar da arziki da kuma ci gaba mai ɗorewa a Jihar Nasarawa.

Manoma 352 da suka amfana an zaɓo su ne daga kananan hukumomi biyar da shirin ya shafa a jihar, da suka hada da Lafiya, Nasarawa, Doma, Karu da Wamba.

Kayayyakin da aka raba sun haɗa da buhunan iri shinkafa mai  nauyin kilo 9,600, da buhunan 1,408 takin NPK 1,408, da buhuna 384 na takin Urea, da lita 352 na maganin ciyawa mara zaɓi, da lita 352 na maganin ciyawa mai zaɓi, da kuma rassa 8,000 na rogo domin dashe.

Haka kuma, an raba mashin mai kafa uku guda tara ga wasu manoma domin sauƙaƙe musu jigilar kayan gona zuwa kasuwa, wanda hakan zai taimaka wajen rage asarar bayan girbi.

Dr. Adgidzi ta jaddada cewa haɗin gwiwar Gwamnatin Tarayya da IFAD da gwamnatin jihar, na nuna jajircewar samar wa manoma kayan aikin da za su taimaka musu wajen samun nasara.

A nasa jawabin, Kwamishinan Noma na Jihar Nasarawa, Alhaji Umaru Tanko Tunga, ya bayyana cewa wannan shiri zai ƙara samar da abinci, rage asarar bayan girbi da kuma inganta rayuwar kananan manoma.

Ya shawarci manoman da suka amfana da su yi amfani da kayayyakin yadda ya kamata, sannan ya yaba wa Gwamna Abdullahi Sule bisa samar da yanayin da ya ba da damar nasarar shirye-shiryen noman a jihar.

A martanin su, wasu daga cikin manoman da suka amfana kamar su Lazarus Okwugya daga Assakio, da Joseph Abimiku da Fatima Shuaibu daga unguwar Azuba, sun nuna godiya ga shirin VCDP bisa irin tallafin da ya kawo, wanda suka ce ya inganta yawan amfanin gona da kuma rayuwarsu.

 

Daga Aliyu Muraki

 

 

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara