Labarai
Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege
Daga Aliyu Muraki
Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar Udege da ke ƙaramar hukumar Nasarawa ta jihar.
Kwamishinan Kananan Hukumomi, Harkokin Masarautu da cigaban Al’umma na jihar, Alhaji Aminu Mu’azu Maifata ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a Lafia, babban birnin jihar.
Ya ce sabon basaraken zai fara aiki ne nan take, yana mai taya shi murna da kuma masa fatan alheri bisa nauyin da aka damka masa.
Alhaji Aminu Mu’azu Maifata ya kuma bayyana cewa an gudanar da nadin ne bayan tattaunawa da Majalisar Sarakunan Gargajiya ta jihar.
Ya ƙara da cewa Suleiman Ahmed Eko ya gaji marigayi Alhaji Halilu Bala-Usman tsohon mataimakin gwamnan tsohuwar Jihar Plateau, wanda ya rasu a ranar Lahadi, 25 ga watan Mayun 2025.
An haifi sabon basaraken ne ranar 2 ga watan Yunin 1972, ya kuma kammala karatunsa ne a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Tarayya da ke Nasarawa. Haka kuma yana da aure tare da ’ya’ya.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
