Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Published

on

Daga Aminu Dalhatu

Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri ga Jami’ar Jiha da ke Talata Mafara, a wani bangare na kokarin inganta saukin shiga makarantar ga dalibai.

Gwamnan jihar, Dakta Dauda Lawal, ya bayyana hakan yayin jawabin da ya gabatar a bikin karbar sabbin dalibai karo na biyar da aka gudanar a harabar jami’ar da ke Talata Mafara, a karamar hukumar Talata Mafara ta jihar.

Gwamnan, wanda mataimakinsa Mani Malam Mummuni ya wakilta, ya jaddada cewa gwamnatinsa ta ayyana dokar ta-baci a bangaren ilimi, kuma tana da kudurin samar da kayayyakin fasaha na zamani domin tabbatar da ingantaccen ilimi a jami’ar.

Gwamna Lawal ya kuma bayyana godiyarsa ga abokan hulda na jami’ar, ciki har da TETFUND, shirin tallafin Gwamnatin Tarayya, da sauransu, bisa hadin gwiwar da suke bayarwa wajen tafiyar da jami’ar cikin nasara.

Ya taya sabbin daliban murnar samun gurbin karatu, tare da gargadinsu da su guji magudin jarabawa, shiga kungiyar asiri, shan miyagun kwayoyi, da sauran dabi’un da za su iya kawo cikas ga karatunsu.

Tun da farko, Shugaban Jami’ar Farfesa Abdullahi Ibrahim Tsafe, ya bayyana cewa dalibai 980 aka karba a zangon karatu na shekarar 2025/2026.

Farfesa Tsafe ya kuma nuna godiya ga gwamnatin jihar bisa dora masa nauyin jagorancin jami’ar, tare da tabbatar da cewa zai yi iya kokarinsa wajen cika amanar da aka dora masa.

Ya kuma bayyana wasu nasarorin da jami’ar ta samu, tare da kalubalen da ke bukatar a magance su.

Sarkin Mafara, Alhaji Bello Muhammad Barmo, shi ma ya yi jawabi a wajen taron, inda ya jaddada muhimmancin neman ilimi ga kowa, tare da yin nuni da ayoyi da hadisai na Manzon Allah (SAW) da ke nuna darajar ilimi.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara