Ilimi
Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara
Daga Aminu Dalhatu
Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri ga Jami’ar Jiha da ke Talata Mafara, a wani bangare na kokarin inganta saukin shiga makarantar ga dalibai.
Gwamnan jihar, Dakta Dauda Lawal, ya bayyana hakan yayin jawabin da ya gabatar a bikin karbar sabbin dalibai karo na biyar da aka gudanar a harabar jami’ar da ke Talata Mafara, a karamar hukumar Talata Mafara ta jihar.

Gwamnan, wanda mataimakinsa Mani Malam Mummuni ya wakilta, ya jaddada cewa gwamnatinsa ta ayyana dokar ta-baci a bangaren ilimi, kuma tana da kudurin samar da kayayyakin fasaha na zamani domin tabbatar da ingantaccen ilimi a jami’ar.
Gwamna Lawal ya kuma bayyana godiyarsa ga abokan hulda na jami’ar, ciki har da TETFUND, shirin tallafin Gwamnatin Tarayya, da sauransu, bisa hadin gwiwar da suke bayarwa wajen tafiyar da jami’ar cikin nasara.
Ya taya sabbin daliban murnar samun gurbin karatu, tare da gargadinsu da su guji magudin jarabawa, shiga kungiyar asiri, shan miyagun kwayoyi, da sauran dabi’un da za su iya kawo cikas ga karatunsu.
Tun da farko, Shugaban Jami’ar Farfesa Abdullahi Ibrahim Tsafe, ya bayyana cewa dalibai 980 aka karba a zangon karatu na shekarar 2025/2026.

Farfesa Tsafe ya kuma nuna godiya ga gwamnatin jihar bisa dora masa nauyin jagorancin jami’ar, tare da tabbatar da cewa zai yi iya kokarinsa wajen cika amanar da aka dora masa.
Ya kuma bayyana wasu nasarorin da jami’ar ta samu, tare da kalubalen da ke bukatar a magance su.
Sarkin Mafara, Alhaji Bello Muhammad Barmo, shi ma ya yi jawabi a wajen taron, inda ya jaddada muhimmancin neman ilimi ga kowa, tare da yin nuni da ayoyi da hadisai na Manzon Allah (SAW) da ke nuna darajar ilimi.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
