Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da ruwa, hanyoyi da kuma wutar lantarki mai amfani da hasken rana ga Jami’ar Tarayya ta Dutse (FUD) da ke Jihar Jigawa.

Ministan ya bayyana hakan ne lokacin da Shugaban Jami’ar, Farfesa Ahmad Muhammad Gumel, tare da tawagarsa suka kai masa ziyarar ban girma a Abuja.

 

Barrista Goronyo ya taya shugaban jami’ar murnar nadin da aka yi masa, inda ya ce FUD jami’a ce mai tasowa wadda ke bukatar goyon bayan  masu ruwa da tsaki domin ta cimma nasara. Ya kara da cewa ilimi yana daga cikin manyan manufofin “Sabunta kudurori” na Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, domin ilimi shi ne ginshikin cigaban al’umma.

Ya ce zai mika bukatar shugaban jami’ar dangane da hanyoyi ga Babban Ministan Ayyuka, Injiniya David Umahi, sannan a matsayinsa na mai kula da Hukumar Kula da Gyaran Hanyoyi ta Tarayya (FERMA), zai yi kokarinsa wajen taimakawa wannan sabuwar jami’a. Ya kuma kara da cewa zai tuntubi Ministan Albarkatun Ruwa domin taimaka wa jami’ar da ayyukan ruwa don saukaka rayuwar dalibai.

Haka kuma, Barrista Goronyo ya shaida wa shugaban jami’ar cewa zai dauki batun samar da lantarki mai amfani da hasken rana tare da Hukumar Samar da Wutar Lantarki a Karkara (REA), inda gwamnati ke kokarin magance matsalar wutar lantarki ta hanyar wasu shirye-shiryen gwaji a manyan makarantun gaba da sakandare.

Ministan ya karfafa wa shugaban jami’ar gwiwa da ya rika ziyartar sauran ma’aikatu da hukumomi domin neman hadin gwiwa da goyon baya don bunkasa wannan sabuwar jami’a.

Tun da farko, a nasa jawabin, Farfesa Gumel ya gode wa Ministan bisa karbar su, yana mai cewa FUD jami’a ce mai tasowa wadda ke bukatar tallafi musamman a fannoni kamar hanyoyi, dakunan kwanan dalibai, ruwa da wutar lantarki.

Ya ce duk da karancin shekarun jami’ar, tana daga cikin mafi nagarta a cikin jami’o’in da tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan ya kafa, har ma tana zarce wasu tsofaffin jami’o’i a wasu fannoni.

Ya yaba da irin nasarorin da Ministan ya samu tun bayan hawansa kan mulki, tare da addu’ar Allah Ya ba shi nasara a dukkan ayyukansa.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara