Labarai
‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara
Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto wasu da aka sace tare da cafke wasu da ake zargi da aikata laifuka.
A wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Yazid Abubakar ya fitar, ya ce da misalin ƙarfe biyu na dare ‘yan bindiga sun kai hari gidan wani ma’aikacin Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta tarayya dake Kaura Namoda, Mamuda Buhari, inda suka sace shi tare da ‘ya’yansa uku.
Sai dai bayan samun rahoton lamarin, jami’an ‘yan sanda tare da hadin gwiwar ‘yan sa-kai suka bi sawun maharan, lamarin da ya kai ga ceto yaran uku, waɗanda aka mayar da su ga iyalansu.
Sanarwar ta ce ana ci gaba da kokarin ceto mutumin da har yanzu yake hannun maharan.
A wani lamari na daban kuma, ‘yan sanda sun cafke mutane biyu da ake zargi da zama ‘yan bindiga bayan sun kai hari ga jami’an tsaro a yankin Mada da ke ƙaramar hukumar Gusau, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbi.
Rundunar ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da farautar waɗanda suka tsere tare da rusa kungiyoyin masu aikata laifi, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin taimakawa yaƙi da ta’addanci.
Aminu Dalhatu/Gusau
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
