Labarai
Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai cewa sabbin gyare-gyaren da gwamnatinsa ta kawo za su samar da dama da wadata ga al’umma.
Ya bayyana haka ne a Abuja yayin kaddamar da sabon hedikwatar Hukumar Haraji ta ƙasa, inda ya jaddada cewa tsarin harajin da aka ƙirƙira yanzu ya fi karkata ga jama’a da kuma jawo zuba jari.
Shugaban ya ce sabbin dokokin, da aka fara aiwatar da su a watan Janairu, za su gyara matsalolin tsohon tsarin tare da sanya tattalin arzikin ƙasar ya zama mai gasa a duniya.

A wajen taron, shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas sun yabawa gyare-gyaren, suna cewa sun fara haifar da sakamako mai kyau.
Shugaban ya kuma buƙaci hukumar haraji ta kasance mai gaskiya da inganci wajen aikinta, tare da gina amincewar jama’a, yana mai cewa hakan ne zai tabbatar da ci gaban tattalin arzikin ƙasa.
Bello Wakili Abuja
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
