Labarai
NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara
Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce wa jihar.
Sabon kwamandan hukumar, Abbas Mohammed, ya bayyana haka a cikin wani saƙo da ya aikewa al’ummar jihar, inda ya jaddada kudurin hukumar na kare rayuka da dukiyoyi da kuma kiyaye muhimman kadarorin ƙasa.
Ya ce rundunar za ta ƙara ƙaimi wajen amfani da hanyoyin tattara bayanan sirri domin yaƙi da dukkan nau’o’in laifuka, tare da ɗaukar matakan rigakafi kafin aukuwar su.
Kwamandan ya kuma nuna cewa jihar Kwara ba za ta zama mafakar masu laifi ba, yana mai cewa a shirye suke su yi amfani da dukkan dabarun tsaro domin tabbatar da zaman lafiya.
Haka kuma, ya buƙaci al’umma da su kasance cikin shiri tare da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai a kan lokaci domin taimakawa yaƙi da aikata laifuka.
Muhammadu Rabi’u/Kwara
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
