Labarai
Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
Daga Bello Wakili
Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da ya faru a ƙaramar hukumar Shanga ta Jihar Kebbi cewa za ta ci gaba da kula da walwalarsu.
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ne ya bayar da wannan tabbaci a Birnin Kebbi yayin ziyarar ta’aziyya da ya kai wa Gwamna Nasir Idris, biyo bayan kisan jami’an tsaro goma sha ɗaya da kuma rasuwar Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, Muhammad Usman Zuru, a birnin Alkahira na ƙasar Masar.
Mataimakin Shugaban Ƙasa, wanda ya jagoranci tawagar Gwamnatin Tarayya a madadin Shugaba Bola Tinubu, ya ce sadaukarwar jami’an da suka rasu ba za ta tafi a banza ba, yana mai jaddada cewa walwalar jami’an tsaro da iyalansu na daga cikin manyan abubuwan da gwamnati ta sa a gaba.
Ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa ya umurci Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da ta samar da tallafin agaji ga iyalan da abin ya shafa da kuma al’ummomin da suka rasa matsugunansu.
Kashim Shettima ya yi addu’ar Allah ya gafarta wa waɗanda suka rasu, tare da yin faran alkhairi ga al’ummar jihar.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
