Labarai
Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi
Daga Sani Dutsinma
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar jihar bisa rasuwar Shugaban Majalisar Dokoki ta Jiha, Muhammad Usman Zuru, da kuma hare-haren ‘yan bindiga a Ƙaramar Hukumar Shanga.
Ya isar da saƙon ta’aziyyar Shugaba Bola Ahmed Tinubu, inda ya bayyana abubuwan da suka faru a matsayin babban rashi ga Jihar Kebbi da ƙasa baki ɗaya. Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafarta wa marigayi Shugaban Majalisa, ya kuma ba iyalansa haƙurin jure wannan babban rashi.

Shettima ya kuma nuna alhini kan hare-haren da aka kai ƙauyukan Gebe, Kalkami, Tungar Rimi da Awaye, wanda ya haddasa asarar rayuka da lalata dukiya, ciki har da sojoji goma sha ɗaya da suka rasa rayukansu yayin aikin tsaro.
Ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya, ta hannun Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Kasa NEMA, za ta tallafa wa waɗanda suka rasa matsugunansu tare da samar da agaji ga al’ummomin da abin ya shafa.

Mataimakin shugaban ƙasa ya kuma yaba wa Gwamna Nasir Idris bisa ƙoƙarinsa wajen ci gaban ilimi, ababen more rayuwa da kuma haɗa kan al’umma a jihar Kebbi.
A nasa bangaren, Sarkin Zuru, Muhammad Sanusi Mikaili Gomo III, ya gode wa tawagar gwamnatin tarayya bisa ziyarar ta’aziyyar da tallafi ga iyalai da al’ummomin da abin ya shafa.

Haka zalika, shi ma Gwamna Nasir Idris kuma ya gode wa Shugaba Tinubu bisa turo tawaga, tare da bayyana cewa gwamnatin jihar ta kafa kwamiti da kuma ware kuɗi domin sake tsugunar da waɗanda suka rasa matsugunni da kuma tallafa wa iyalan sojojin da suka rasu.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
