Connect with us

Labarai

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Published

on

Daga Sani Dutsinma

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar jihar bisa rasuwar Shugaban Majalisar Dokoki ta Jiha, Muhammad Usman Zuru, da kuma hare-haren ‘yan bindiga a Ƙaramar Hukumar Shanga.

Ya isar da saƙon ta’aziyyar Shugaba Bola Ahmed Tinubu, inda ya bayyana abubuwan da suka faru a matsayin babban rashi ga Jihar Kebbi da ƙasa baki ɗaya. Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafarta wa marigayi Shugaban Majalisa, ya kuma ba iyalansa haƙurin jure wannan babban rashi.

Shettima ya kuma nuna alhini kan hare-haren da aka kai ƙauyukan Gebe, Kalkami, Tungar Rimi da Awaye, wanda ya haddasa asarar rayuka da lalata dukiya, ciki har da sojoji goma sha ɗaya da suka rasa rayukansu yayin aikin tsaro.

Ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya, ta hannun Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Kasa NEMA, za ta tallafa wa waɗanda suka rasa matsugunansu tare da samar da agaji ga al’ummomin da abin ya shafa.

Mataimakin shugaban ƙasa ya kuma yaba wa Gwamna Nasir Idris bisa ƙoƙarinsa wajen ci gaban ilimi, ababen more rayuwa da kuma haɗa kan al’umma a jihar Kebbi.

A nasa bangaren, Sarkin Zuru, Muhammad Sanusi Mikaili Gomo III, ya gode wa tawagar gwamnatin tarayya bisa ziyarar ta’aziyyar da tallafi ga iyalai da al’ummomin da abin ya shafa.

Haka zalika, shi ma Gwamna Nasir Idris kuma ya gode wa Shugaba Tinubu bisa turo tawaga, tare da bayyana cewa gwamnatin jihar ta kafa kwamiti da kuma ware kuɗi domin sake tsugunar da waɗanda suka rasa matsugunni da kuma tallafa wa iyalan sojojin da suka rasu.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara