Kasuwanci
Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
Daga Aliyu Lawal
Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa da aka fi sani da ‘yan gwangwan a cikin Unguwanni.
An amince da kudirin dokar ne yayin zaman majalisa da aka gudanar a harabar majalisar da ke Minna.
Amincewar ta biyo bayan gabatarwa da kuma karɓar rahoton hadin gwiwar kwamitocin majalisar kan Muhalli da Sauyin Yanayi, Shari’a da Harkokin Doka.
Yayin gabatar da rahoton, shugaban kwamitocin hadin gwiwa, Mohammed Garba, mai wakiltar mazabar Agwara, ya bayyana cewa kwamitocin sun gudanar da zaman sauraron ra’ayoyin jama’a inda suka gayyaci masu ruwa da tsaki domin gabatar da nasu ra’ayoyin.
Ya ce an gudanar da wannan tattaunawa ne sakamakon karuwar damuwa kan barazanar tsaro, illa ga muhalli, da matsalolin zaman lafiya da suka shafi ayyukan baban bola da kasuwancin karafa ba tare da tsari ba a cikin unguwanni a fadin jihar.
Rahoton ya nuna cewa an tsara kudirin dokar ne domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma, inganta tsaron jama’a, da kuma tsara harkokin sana’ar karafa da “Panteka” ta hanyar mayar da su wurare na musamman da aka ware a wajen unguwannin.
Haka kuma kwamitocin sun lura cewa ayyukan wadanda aka fi sani da Baban bola da ‘yan kasuwar karafa na da alaka da karuwar sace-sace da lalata kadarorin gwamnati da na jama’a.
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
