Connect with us

Kasuwanci

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Published

on

Daga Aliyu Lawal 

Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa da aka fi sani da ‘yan gwangwan a cikin Unguwanni.

An amince da kudirin dokar ne yayin zaman majalisa da aka gudanar a harabar majalisar da ke Minna.

Amincewar ta biyo bayan gabatarwa da kuma karɓar rahoton hadin gwiwar kwamitocin majalisar kan Muhalli da Sauyin Yanayi, Shari’a da Harkokin Doka.

Yayin gabatar da rahoton, shugaban kwamitocin hadin gwiwa, Mohammed Garba, mai wakiltar mazabar Agwara, ya bayyana cewa kwamitocin sun gudanar da zaman sauraron ra’ayoyin jama’a inda suka gayyaci masu ruwa da tsaki domin gabatar da nasu ra’ayoyin.

Ya ce an gudanar da wannan tattaunawa ne sakamakon karuwar damuwa kan barazanar tsaro, illa ga muhalli, da matsalolin zaman lafiya da suka shafi ayyukan baban bola da kasuwancin karafa ba tare da tsari ba a cikin unguwanni a fadin jihar.

Rahoton ya nuna cewa an tsara kudirin dokar ne domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma, inganta tsaron jama’a, da kuma tsara harkokin sana’ar karafa da “Panteka” ta hanyar mayar da su wurare na musamman da aka ware a wajen unguwannin.

Haka kuma kwamitocin sun lura cewa ayyukan wadanda aka fi sani da Baban bola da ‘yan kasuwar karafa na da alaka da karuwar sace-sace da lalata kadarorin gwamnati da na jama’a.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara