Connect with us

Labarai

An Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni

Published

on

Daga Khadijah Aliyu

Yara kimanin 66,446 ne  aka yi wa rigakafin cutar shan inna wato polio, a  Karamar Hukumar Tarauni, wanda hakan ya zama babbar nasara a ƙoƙarin da ake yi na kawar da cutar baki ɗaya.

Mai kula da harkokin lafiya na matakin farko a yankin, Muktar Datti Gwarzo, ya danganta wannan nasara da goyon bayan al’umma da haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki.

Ya bayyana cewa jajircewar shugabannin gargajiya, ma’aikatan lafiya, da shugabannin ƙaramar hukuma ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da cewa an yi wa dukkan yaran da suka cancanta wannan rigakafi.

Gwarzo ya ƙara da cewa za a ci gaba da ƙarfafa wayar da kan jama’a domin ilmantar da su muhimmancin yin rigakafi a kai a kai, da nufin kawar da cutar polio gaba ɗaya a yankin.

Shi ma da yake jawabi, mai wayar da kan jama’a kan harkokin lafiya, Musa Abdullahi Shamakawa, ya yaba da ƙwazon ma’aikatan lafiya da sarakunan gargajiya wajen wayar da kan iyaye kan amfanin rigakafi.

A nasa bangaren, Daraktan kula da ma’aikata na ƙaramar hukuma kuma Shugaban Ƙungiyar Daraktocin Ƙananan Hukumomi 44, Tijjani Madaki Gulya, ya buƙaci iyaye da masu kula da yara da su ci gaba da goyon bayan shirye-shiryen rigakafi domin kare lafiyar yara da al’umma baki ɗaya.

Ya jaddada cewa ci gaba da shiga irin waɗannan shirye-shirye yana da matuƙar muhimmanci wajen hana yaduwar cututtukan da za a iya rigakafinsu.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara