Connect with us

Labarai

  Kwara: Shugabannin APC na Mazabu 52 sun amince da Abdulrazaq a takarar Sanata 2027

Published

on

Shugabannin ƙananan hukumomi na jam’iyyar APC a yankin Kwara Ta Tsakiya sun amince gaba ɗaya da Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq a matsayin ɗan takarar Sanata mai wakiltar mazabar a zaɓen 2027.

Shugabannin Ward 52 ne suka bayyana haka yayin ganawa da ‘yan jarida a Ilorin ƙarƙashin inuwar kungiyar Sugabbanin Mazabun APC, wanda shugaban su, Alhaji Abdullahi Baba Gobir, ya jagoranta.

Sun ce Abdulrazaq ya fi kowa sanin bukatu da muradun al’ummar yankin Kwara Ta Tsakiya, kasancewarsa ɗan asalin yankin kuma mai kusanci da jama’a.

A cewarsu, wannan goyon baya ya samo asali ne daga ra’ayin tabbatar da jin daɗin jama’a da ci gaban yankin Kwara Central.

Sun ƙara da cewa matakin ya kuma dace da al’adar siyasa ta ba shugabanni damar ci gaba da hidima a mataki mafi girma idan sun nuna ƙwazo a shugabanci.

Shugabannin sun jaddada cewa goyon bayan ba siyasa kawai ba ne, illa dai ra’ayi ne na haɗin kai domin tabbatar da ci gaba da shugabanci nagari da zai amfanar da jama’a a matakin ƙasa.

Ali Muhammad Rabiu/Ilorin

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara