Labarai
Kwara: Shugabannin APC na Mazabu 52 sun amince da Abdulrazaq a takarar Sanata 2027
Shugabannin ƙananan hukumomi na jam’iyyar APC a yankin Kwara Ta Tsakiya sun amince gaba ɗaya da Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq a matsayin ɗan takarar Sanata mai wakiltar mazabar a zaɓen 2027.
Shugabannin Ward 52 ne suka bayyana haka yayin ganawa da ‘yan jarida a Ilorin ƙarƙashin inuwar kungiyar Sugabbanin Mazabun APC, wanda shugaban su, Alhaji Abdullahi Baba Gobir, ya jagoranta.
Sun ce Abdulrazaq ya fi kowa sanin bukatu da muradun al’ummar yankin Kwara Ta Tsakiya, kasancewarsa ɗan asalin yankin kuma mai kusanci da jama’a.
A cewarsu, wannan goyon baya ya samo asali ne daga ra’ayin tabbatar da jin daɗin jama’a da ci gaban yankin Kwara Central.
Sun ƙara da cewa matakin ya kuma dace da al’adar siyasa ta ba shugabanni damar ci gaba da hidima a mataki mafi girma idan sun nuna ƙwazo a shugabanci.
Shugabannin sun jaddada cewa goyon bayan ba siyasa kawai ba ne, illa dai ra’ayi ne na haɗin kai domin tabbatar da ci gaba da shugabanci nagari da zai amfanar da jama’a a matakin ƙasa.
Ali Muhammad Rabiu/Ilorin
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
