Connect with us

Ilimi

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

Published

on

 

By Adamu Yusuf

 

Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan tsaftace bayanai da rubuta rahotanni da zai taimaka wajen rage karuwar yawan yara da basu zuwa makaranta a cikin al’ummomin makiyaya a kasar nan.

 

Babban Daraktan a Hukumar, Dr. Abdu Umar Hardo, ya bayyana hakan yayin bude taron da aka gudanar a hedkwatar hukumar dake Kaduna.

 

Dr. Umar Hardo ya ce horon yana karkashin hadin gwiwa ne tsakanin Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da Hukumar Ilimantar da Makiyaya ta kasa da Hukumar Ilimin da Al-Majirai da Hukumar Ilimintar da Jama’a (NCME) da dai sauransu.

Ya kara da cewa shirin yana nufin baiwa ma’aikata kwarewa wajen nazari da sarrafa bayanan da aka tattara da aka samo domin aiwatar da shirye-shiryen don rage yawan yaran makiyaya da basa zuwa makaranta.

 

Dr. Hardo ya ce hukumar an dora mata alhakin rage yawan yara da basu zuwa makaranta ba a cikin al’ummomin makiyaya kawai ba har da masu kamun kifi da manoma a fadin kasar.

 

A cewarsa, kimanin yara miliyan 5.5 daga al’ummomin makiyaya ba sa zuwa makaranta a yayin da kimanin yara miliyan 1.5 ke halartar makaranta, lamarin da ke nuna babban gibi da shirin ke nufin magancewa.

 

Ya kara da cewa kwanan nan hukumar ta gudanar da binciken taswira a jihohi shida da Babban Birnin Tarayya (FCT), ciki har da Jigawa, Gombe, Nasarawa, Enugu, Cross River, da Oyo, inda aka gano kimanin yara da matasa 660,000 da basu zuwa makaranta ba.

 

A jawabin sa, Professor Aminu Abdul Bichi, kwararre daga African Institute for Solution Development, ya ce horon ya mayar da hankali ne kan kididigar bayanai da aka samu wanda hakan zai taimaka wajen tsara yanda za’a dawo dasu makaranta.

 

Professor Bichi ya bayyana cewa nazarin bayanai ya nuna cewa kimanin kashi 62 cikin 100 na yara makiyaya ba su zuwa makaranta, yayin da kashi 32 cikin 100 suka daina zuwa makaranta a matakin firamare.

 

Ya kara da cewa 3.2 cikin 100 sun daina makaranta a matakin sakandare na farko, yayin da 1.2 cikin 100 suka daina a sakandare na gaba.

 

Professor Bichi ya ce wadannan bayanai sun nuna babbar matsalar kuma suna nuni da bukatar shirye-shirye na musamman da suka dogara da bayanai domin tabbatar da cewa yara daga al’ummomin makiyaya suna samun damar ilimi.

 

A ganawa da Radio Nigeria, Daraktar Tsare-Tsare, Bincike da Kididdiga a Hukumar, Dr. Rose Nkechi Nwaji, ta ce rungumar Shirin Ilimin Firamare Na musamman zai taimaka wajen rage yawan yara da basu zuwa makaranta musamman a cikin al’ummomin makiyaya.

 

Dr. Nwaji ta ce shirin, zai baiwa yara da suka daina zuwa makarantar damar karatu domin su shiga tsarin ilimi na kasa.

Ana sa ran mahalarta horon za su nazarci bayanan da aka tattara domin amfanin da su wajen tsara manufofi da za’a yi amfani dasu wajen maganin matsalar rashin zuwa makaranta na yaran makiyaya ta amfanin da sabon Shirin Ilimin Firamare na (ABEP).

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci7 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara