Ilimi
Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta
By Adamu Yusuf
Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan tsaftace bayanai da rubuta rahotanni da zai taimaka wajen rage karuwar yawan yara da basu zuwa makaranta a cikin al’ummomin makiyaya a kasar nan.
Babban Daraktan a Hukumar, Dr. Abdu Umar Hardo, ya bayyana hakan yayin bude taron da aka gudanar a hedkwatar hukumar dake Kaduna.
Dr. Umar Hardo ya ce horon yana karkashin hadin gwiwa ne tsakanin Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da Hukumar Ilimantar da Makiyaya ta kasa da Hukumar Ilimin da Al-Majirai da Hukumar Ilimintar da Jama’a (NCME) da dai sauransu.

Ya kara da cewa shirin yana nufin baiwa ma’aikata kwarewa wajen nazari da sarrafa bayanan da aka tattara da aka samo domin aiwatar da shirye-shiryen don rage yawan yaran makiyaya da basa zuwa makaranta.
Dr. Hardo ya ce hukumar an dora mata alhakin rage yawan yara da basu zuwa makaranta ba a cikin al’ummomin makiyaya kawai ba har da masu kamun kifi da manoma a fadin kasar.
A cewarsa, kimanin yara miliyan 5.5 daga al’ummomin makiyaya ba sa zuwa makaranta a yayin da kimanin yara miliyan 1.5 ke halartar makaranta, lamarin da ke nuna babban gibi da shirin ke nufin magancewa.
Ya kara da cewa kwanan nan hukumar ta gudanar da binciken taswira a jihohi shida da Babban Birnin Tarayya (FCT), ciki har da Jigawa, Gombe, Nasarawa, Enugu, Cross River, da Oyo, inda aka gano kimanin yara da matasa 660,000 da basu zuwa makaranta ba.
A jawabin sa, Professor Aminu Abdul Bichi, kwararre daga African Institute for Solution Development, ya ce horon ya mayar da hankali ne kan kididigar bayanai da aka samu wanda hakan zai taimaka wajen tsara yanda za’a dawo dasu makaranta.
Professor Bichi ya bayyana cewa nazarin bayanai ya nuna cewa kimanin kashi 62 cikin 100 na yara makiyaya ba su zuwa makaranta, yayin da kashi 32 cikin 100 suka daina zuwa makaranta a matakin firamare.
Ya kara da cewa 3.2 cikin 100 sun daina makaranta a matakin sakandare na farko, yayin da 1.2 cikin 100 suka daina a sakandare na gaba.
Professor Bichi ya ce wadannan bayanai sun nuna babbar matsalar kuma suna nuni da bukatar shirye-shirye na musamman da suka dogara da bayanai domin tabbatar da cewa yara daga al’ummomin makiyaya suna samun damar ilimi.
A ganawa da Radio Nigeria, Daraktar Tsare-Tsare, Bincike da Kididdiga a Hukumar, Dr. Rose Nkechi Nwaji, ta ce rungumar Shirin Ilimin Firamare Na musamman zai taimaka wajen rage yawan yara da basu zuwa makaranta musamman a cikin al’ummomin makiyaya.
Dr. Nwaji ta ce shirin, zai baiwa yara da suka daina zuwa makarantar damar karatu domin su shiga tsarin ilimi na kasa.

Ana sa ran mahalarta horon za su nazarci bayanan da aka tattara domin amfanin da su wajen tsara manufofi da za’a yi amfani dasu wajen maganin matsalar rashin zuwa makaranta na yaran makiyaya ta amfanin da sabon Shirin Ilimin Firamare na (ABEP).
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci7 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
