Connect with us

Labarai

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

Published

on

 

Daga Khadija Kubau

 

Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba magunguna domin kare al’umma daga kamuwa daga cutar dundumi River Blindness a jihar.

 

An gudanar da bikin kaddamar da shirin ne a Cibiyar Kula da Lafiya ta Matakin Farko (PHC) da ke Kinkinau a Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu, inda jami’an lafiya da shugabannin al’umma da kuma abokan hulɗa suka halarta domin tallafawa yaki da cututtukan da aka yi watsi da su wato Neglected Tropical Diseases

 

Kwamishinar Lafiya ta Jihar, Hajiya Umma K. Ahmed, wadda ta kaddamar da shirin rabon magungunan, ta bayyana cewa za a gudanar da shirin ne a kananan hukumomi shida daga cikin kananan hukumomi 23 na jihar.

 

Kwamishinar, wadda Daraktan Kiwon Lafiyar Jama’a, Dakta Abubakar Sadiq Idris ya wakilta, ta ce an zabi Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu ne domin fara shirin saboda bincike ya nuna cewa akwai mutane da dama da cutar ta fi shafa a yankin.

 

Ta kara da cewa za a raba magungunan ga mutane masu shekaru biyar zuwa sama domin dakile yaduwar cutar tare da rage illolinta a cikin al’umma.

 

Da take jawabi a wajen taron, Madam Gong, wadda ta wakilci Daraktar kungiyar Sightsavers Nigeria, Farfesa Joy Shuaibu, ta roki al’umma da su rika shan magungunan kamar yadda jami’an lafiya suka umarta.

 

Ta jaddada cewa hadin kan al’umma yana da matukar muhimmanci wajen cimma burin kawar da cutar.

 

Tun da farko, jami’ar kulada Cututtukan da aka yi watsi da su, (NTD), Zainab Haruna, ta bayyana manufofin shirin, inda ta ce an kirkiro shi ne domin rage yawaitar cutar ta hanyar raba magungunan kariya kyauta ga al’umma.

 

Ta kuma bukaci mazauna yankin da su baiwa jami’an lafiya hadin kai tare da halartar shirin domin cin gajiyar magungunan.

 

A nasa jawabin, Daraktan Kiwon Lafiyar Jama’a, Dakta Abubakar Sadiq Idris, ya jaddada kudurin gwamnatin jihar na ci gaba da yakar cututtukan da aka yi watsi da su ta hanyar shirye-shiryen kiwon lafiya da kuma hadin gwiwa da kungiyoyin tallafi.

 

A jawabin maraba, wakilin Shugaban Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu, Dakta Maidubu, ya gode wa Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna da kuma kungiyar Sightsavers bisa tallafinsu ga wannan shiri.

 

Ya tabbatar da cewa za a raba magungunan yadda ya kamata domin tabbatar da cewa duk wadanda suka cancanta sun amfana da shirin.

 

Hakimin Tudun Wada, Alhaji Tahir Mahmud, wanda shi ne Uban Taron, ya yi alkawarin cikakken goyon bayan masarautar gargajiya domin ganin shirin ya yi nasara.

 

Ya kara da cewa za su wayar da kan al’umma tare da karfafa musu gwiwa su fito domin karbar magungunan.

 

Daya daga cikin abubuwan da suka dauki hankalin mahalarta taron shi ne wasan kwaikwayo da aka gabatar domin wayar da kan al’umma kan haddasuwar cutar, hanyoyin kariya, da kuma muhimmancin halartar shirin rabon magungunan.

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci7 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara