Connect with us

Labarai

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Published

on

Daga Sani Dutsinma

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kebbi bayan duba kayayyakin aiki da shirye-shiryen da aka tanada domin gudanar da aikin Hajji cikin nasara.

Shugaban tawagar binciken, Injiniya Abba Shu’aibu Babagana ne ya bayyana hakan yayin ziyarar aiki da ya jagoranta zuwa jihar ta Kebbi.

A yayin ziyarar, jami’an NCAA sun duba muhimman wurare da dama a sansanin Alhazai na Kauran Gwandu Hajj Camp domin tantance yadda aka shirya kafin fara jigilar maniyyata zuwa aikin Hajjin bana.

Sun kuma ziyarci Cibiyar ICT, inda ake gudanar da rajista da sarrafa bayanan maniyyata ta hanyar fasahar zamani.

Hakazalika, tawagar ta duba Dakin Taro da ake amfani da shi wajen gudanar da tarurruka, da kuma Dakin Tantancewa  inda ake  gwajin lafiya, tabbatar da takardu, da sauran matakan tantancewa domin tabbatar da ganin dukkan maniyyata sun cika ka’idojin tafiya kafin a tafi aikin Hajji.

Jami’an NCAA sun kuma zagaya harabar sansanin Alhazan gaba ɗaya, inda suka nuna gamsuwa da tsafta, tsari, da kuma kayayyakin da aka tanada domin tallafawa maniyyata yayin shirye-shiryen tafiya.

A cewar jami’an, kayayyakin more rayuwa da tsare-tsaren da Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kebbi ta samar, na nuna irin ƙoƙarin gwamnatin jihar wajen tabbatar da cewa an gudanar da aikin Hajji cikin tsari, aminci, da inganci.

Ziyarar na daga cikin binciken da hukumar ke yi akai-akai domin tabbatar da cewa jihohi suna bin ƙa’idojin sufurin jiragen sama da ka’idojin aiki da ake buƙata domin nasarar jigilar maniyyata zuwa Saudi Arabia.

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci7 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara