Labarai
Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina
Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin dajin Rugu, wurin da ’yan bindiga ke fakewa a jihohin Katsina da Zamfara.
Daga cikin wadanda aka kashe akwai fitaccen jagoran ’yan bindiga Damale, da kuma Alti, wanda yake mataimaki ga wani jagoran ’yan bindiga mai suna Adamu Alieru.
Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Katsina, Dakta Mu’azu Danmusa, ya ce jami’an tsaro sun samu sahihan bayanai cewa ’yan bindiga na shirin kai hari kan wata al’umma da ta dakile satar shanu a yankin.
Ya ce lamarin ya fara ne a ranar 5 ga Maris lokacin da ’yan bindiga dauke da makamai suka kai hari kauyen Alhazawa a karamar hukumar Musawa domin satar shanu. Sai dai mazauna yankin tare da wasu ’yan bindiga da suka tuba suka fatattake su, inda aka kashe hudu daga cikinsu kuma aka kwato shanun.
Washegari kuma ’yan bindigar suka dawo da yawa domin daukar fansa, amma suka yi karo da sojoji na sansanin Dan-Ali, inda aka yi artabu har sojojin suka kashe dukkanin ’yan bindigar 45.
Kwamishinan ya yabawa sojoji kan kokarinsu, tare da rokon al’umma su ci gaba da bai wa jami’an tsaro bayanan sirri domin kare yankunansu.
Isma’il Adamu/Kastina
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai6 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
