Labarai
Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya
Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin Musulunci da ci gaban jihar ba.
Kwamishinan Harkokin Addini, Muhammad Sani Aliyu, ya bayyana haka yayin wani taron manema labarai a Birnin Kebbi. Ya ce zargin ba shi da tushe, kuma ya biyo bayan wata hudubar Juma’a da Bashir Jega ya yi inda ya soki gwamnati kan harkokin addini.
A cewarsa, daga cikin manyan nasarorin gwamnatin akwai kafa Ma’aikatar Harkokin Addini, wadda ya ce al’ummar jihar suka dade suna fata sama da shekaru 25 ba tare da an cimma ba.
Ya kuma ce gwamnati ta kara karfafa hukumomi kamar Hukumar Zakka da Waqafi, da Hukumar Wa’azi, da kuma Hukumar Hisbah, tare da samar musu dokoki da tallafi domin gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.
Kwamishinan ya bukaci malaman addini su mai da hankali wajen wa’azin zaman lafiya da hadin kai, tare da kauce wa shiga rigingimun siyasa da ka iya yaudarar al’umma.
Sani Haruna/Kebbi
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci7 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
