Labarai
Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki su kara kaimi wajen tallafa wa mata da ’yan mata a fadin jihar.
Ta bayyana hakan ne yayin bikin Ranar Mata ta Duniya, inda ta ce bikin na tunatar da muhimmiyar rawar da mata ke takawa wajen gina iyali, al’umma da kuma ci gaban kasa.
Kwamishinar ta jaddada kudurin ma’aikatar wajen inganta daidaito tsakanin maza da mata, kare hakkin mata da yara, da kuma samar da damar da za ta ba mata damar cimma burinsu.
Ta kuma yabawa Gwamna Abba Kabir Yusuf kan goyon bayan manufofi da shirye-shiryen da ke karfafa mata da kuma kula da marasa karfi a Kano.
A karshe, ta bukaci iyalai da kungiyoyi su kara tallafa wa shirye-shiryen ilimi, kasuwanci da jagoranci ga mata, domin gina al’umma mai adalci inda kowa zai samu dama ba tare da wariya ba.
Khadijah Aliyu/Kano
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci7 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
