Labarai
Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata
Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da kamfanoni masu zaman kansu su hada kai wajen samar da yanayin da zai bai wa mata da ’yan mata damar cimma burinsu.
A sakon da ta fitar domin bikin Ranar Mata ta Duniya ta 2026, Hajiya Huriyya ta ce taken bana “Give to Gain” na nuna muhimmancin zuba jari a kan mata ta hanyar ba su ilimi, horo da damar samun albarkatu.
Ta ce mata na taka muhimmiyar rawa wajen gina iyali, karfafa al’umma da kuma bunkasa tattalin arziki da zamantakewa.
Ta kuma tabbatar da cewa ofishinta zai ci gaba da tallafa wa shirye-shiryen da ke taimaka wa mata da ’yan mata musamman a bangarorin lafiya, ilimi, sana’o’i da walwalar jama’a.
Hajiya Huriyya ta kuma bukaci mata a Zamfara su ci gaba da jajircewa wajen ba da gudunmawa ga ci gaban jihar, tare da amfani da sauran kwanakin Ramadan wajen yi wa Zamfara da Najeriya addu’ar zaman lafiya da ci gaba.
Aminu Dalhatu/Gusau
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai6 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
