Labarai
’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa
Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki a hanyar Gitata zuwa Gunduma a karamar hukumar Keffi.
Cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, SP Ramhan Nansel, ya fitar, ya ce an gano wadanda ake zargin da suna Chigozie Igbokwe da Emmanuel John, dukkansu mazauna Jikwoyi a Abuja.
Sanarwar ta ce an kwato wasu kayayyaki daga hannunsu da suka hada da almakashi na karfe, filaya, mabudai, igiyoyin wuta, da kuma mota kirar Hyundai Sonata mai launin toka mai lambar rajista GWA 44 PM, wadda ake zargin sun yi amfani da ita wajen daukar kayayyakin da suka lalata.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Shatima Jauro Mohammed, ya umarci a mika lamarin zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar a Lafia domin ci gaba da bincike da kuma gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.
Aliyu Muraki/Lafia
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci7 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
