Labarai
NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara
Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka da ’yan bindiga a karamar hukumar Patigi.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Ayoola Ishola, ya fitar, ya ce an kama Abubakar Jubril da Mohammed Abubakar ne bayan wani samame da jami’an tsaro suka kai bisa bayanan sirri.
Sanarwar ta ce an hango mutane uku a wani yanki mai fama da matsalar tsaro, inda aka kama biyu daga cikinsu, yayin da daya ya tsere kuma ake ci gaba da nemansa.
An kuma kwato wasu kayayyaki daga hannun wadanda ake zargin da suka hada da bindiga karama, wayar salula, da wasu kwayoyi da ake zargin Tramadol ne, da kuma taba sigari.
Da yake gabatar da wadanda ake zargin, kwamandan NSCDC a jihar, Bala Bodinga, ya ce hukumar za ta ci gaba da yaki da ayyukan ta’addanci domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Ya kuma gargadi masu aikata laifi su daina, tare da bukatar jama’a su rika bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin taimakawa wajen yaki da laifuka.
Ali Muhammad Rabi’u/Ilorin
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci7 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
