Labarai
Hukumar Shige da Fice ta Kasa ta Ceto Mutane 22 da Aka Yi Yunkurin Safararsu
Daga Isma’il Adamu
Hukumar Shige da Fice ta kasa ta ceto mutane 22 da aka yi yunkurin safararsu, a yankin kan iyakar Zango da ke Jihar Katsina.
Kwamandan Hukumar na Rundunar Iyakokin Jibia, Haruna Zakirai ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudana a Daura.
Ya bayyana cewa an gudanar da aikin ceton ne a sansanin sintirin jami’an hukumar da ke Daura, bayan samun bayanan sirri daga wasu mazauna yankunan da ke kan iyaka, waɗanda yi zargin wadansu mutane yayin da suke ƙoƙarin tsallakawa da waɗanda abin ya shafa zuwa ƙetare.
Zakirai ya ce jami’ai da ma’aikatan sansanin sintiri na Daura sun gaggauta ɗaukar mataki, inda suka tare waɗanda mutanen a wani kango a ƙauyen Maibara da ke Ƙaramar Hukumar Zango ta jihar.
Ya bayyana cewa mutanen da aka ceto sun haɗa da mata 11 da maza 11, masu shekaru tsakanin 17 zuwa 35, waɗanda suka fito daga jihohi daban-daban na ƙasar nan da suka haɗa da Lagos, Osun, Rivers, Kwara, Katsina, Imo, Ondo, Benue, da Babban Birnin Tarayya Abuja.
“Binciken farko ya nuna cewa ana safarar mutanen ne zuwa ƙasar Libya, daga nan kuma zuwa Turai, inda aka yaudare su da alkawarin samun ingantacciyar rayuwa.
“Wannan dabara ce da ƙungiyoyin safarar mutane ke yawan amfani da ita wajen ruɗar mutanen da ba su sani ba. Muna kira ga al’umma da su guji fadawa wannan tarko, domin a koda yaushe Hukumar Shige da Fice tana shirye wajen tarwatsa irin waɗannan ƙungiyoyi da kuma ceto mutanen da ake yunkurin safarar su,” in ji shi.
Zakirai ya ƙara da cewa akwai ɗan ƙasar Togo daga cikin mutanen da aka ceto, wanda za a mayar da shi ƙasarsa bayan kammala bincike. Ya kuma ce a yanzu haka hukumar na neman shugaban ƙungiyar masu safarar wanda aka sani da suna “Cargo” ruwa a jallo, wanda ya tsere lokacin da ake kokarin kama ‘yan ƙungiyar ta sa.
Ya jaddada ƙudirin Hukumar Shige da Fice ta kasa, na yaƙi da safarar mutane, ƙaura ba bisa ƙa’ida ba, da laifukan ketare iyaka, tare da roƙon al’umma da su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai kan duk wani da ake zargi da safarar mutane.
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
