Labarai
Gwamnatin Tarayya ta Nuna Damuwa kan Jinkirin Aikin Hanyar Zariya- Sakkwato
Ministan Ƙasa a ma’aikatar Ayyuka, Bello Muhammad Goronyo, ya bayyana damuwarsa kan jinkirin ci gaban aiki a wani sashe na aikin gina tagwayen hanyar Zariya–Funtuwa–Gusau–Talata Mafara–Sakkwato, inda ya bayyana hanyar a matsayin muhimmin aikin da ya wajaba a kammala cikin gaggawa domin ceto rayuka da bunƙasa harkokin tattalin arziki.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin ziyarar duba aikin da ake ci gaba da yi, wadda aka gudanar bisa umarnin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da kuma Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi.
Da yake zantawa da manema labarai a Kilomita na 16 a kan hanyar Gusau, kusa da Bungudu, Goronyo ya ce ziyarar ta kasance ne domin tantance matakin aikin da kamfanonin da ke kula da sassa daban-daban na hanyar suka aiwatar zuwa yanzu.
Ya bayyana cewa sashen Sakkwato–Talata Mafara, wanda kamfanin CBC Construction Company ke aiwatarwa, mai tsawon kimanin kilomita 105, ya kai kusan kashi 27 cikin 100 na kammala aiki, inda ya yaba da ingancin aikin da ake yi a yankin.
A cewarsa, an taɓa tsallake wasu sassan hanyar ne a baya sakamakon rashin biyan diyya ga al’ummomin da aikin ya shafa, matsalar da ya ce an riga an warware ta.
Bello Goronyo ya bayyana cewa Gwamnan Jihar Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu Sokoto, ya biya sauran diyya da ake bi, inda ya yaba masa ƙwarai bisa goyon bayan da yake bai wa Gwamnatin Tarayya da Shugaban Ƙasa.
Ya ce an umarci kamfanin CBC da ya koma waɗancan sassan da aka tsallake domin kammala su, don tabbatar da cikakkiyar hanya mai laushi ba tare da wata matsala ba.
Sai dai Ministan ya nuna rashin jin daɗi kan yadda aikin ke tafiya a sashen da kamfanin Triacta Nigeria Limited ke gudanarwa, inda ya ce kamfanin ya kai kashi 16 cikin 100 kacal na aiki duk da cewa an ba shi kwangilar a kusan lokaci guda tun Mayun 2023.
“Wannan hanya na da matuƙar muhimmanci. ‘Yan Najeriya na shan wahala. Hatsarori na yawaita, kuma tafiyar daga Sakkwato zuwa Gusau, wadda ya kamata ta ɗauki awa ɗaya da rabi, yanzu tana ɗaukar awanni huɗu zuwa biyar. Wannan ba abin yarda ba ne,” in ji Goronyo.
Ministan ya bayyana cewa lokacin kammala aikin gaba ɗaya an sa shi ne a shekarar 2028, inda ya sake jaddada ƙudirin Gwamnatin Tarayya na gina hanyoyi masu ɗorewa ta amfani da fasahar kankare mai ƙarfe, yana mai danganta lalacewar hanyoyin kwalta da yawan lodin manyan motoci.
A ziyarar, Ministan ya samu rakiyar wasu Daraktoci na Ma’aikatar Ayyuka, da kuma Kontarola na Ma’aikatar Ayyuka a Jihar Zamfara.
AMINU DALHATU
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai6 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
