Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya ta Nuna Damuwa kan Jinkirin Aikin Hanyar Zariya- Sakkwato

Published

on

Ministan Ƙasa a ma’aikatar Ayyuka, Bello Muhammad Goronyo, ya bayyana damuwarsa kan jinkirin ci gaban aiki a wani sashe na aikin gina tagwayen hanyar Zariya–Funtuwa–Gusau–Talata Mafara–Sakkwato, inda ya bayyana hanyar a matsayin muhimmin aikin da ya wajaba a kammala cikin gaggawa domin ceto rayuka da bunƙasa harkokin tattalin arziki.

Ministan ya bayyana hakan ne yayin ziyarar duba aikin da ake ci gaba da yi, wadda aka gudanar bisa umarnin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da kuma Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi.

Da yake zantawa da manema labarai a Kilomita na 16 a kan hanyar Gusau, kusa da Bungudu, Goronyo ya ce ziyarar ta kasance ne domin tantance matakin aikin da kamfanonin da ke kula da sassa daban-daban na hanyar suka aiwatar zuwa yanzu.

Ya bayyana cewa sashen Sakkwato–Talata Mafara, wanda kamfanin CBC Construction Company ke aiwatarwa, mai tsawon kimanin kilomita 105, ya kai kusan kashi 27 cikin 100 na kammala aiki, inda ya yaba da ingancin aikin da ake yi a yankin.

A cewarsa, an taɓa tsallake wasu sassan hanyar ne a baya sakamakon rashin biyan diyya ga al’ummomin da aikin ya shafa, matsalar da ya ce an riga an warware ta.

Bello Goronyo ya bayyana cewa Gwamnan Jihar Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu Sokoto, ya biya sauran diyya da ake bi, inda ya yaba masa ƙwarai bisa goyon bayan da yake bai wa Gwamnatin Tarayya da Shugaban Ƙasa.

Ya ce an umarci kamfanin CBC da ya koma waɗancan sassan da aka tsallake domin kammala su, don tabbatar da cikakkiyar hanya mai laushi ba tare da wata matsala ba.

Sai dai Ministan ya nuna rashin jin daɗi kan yadda aikin ke tafiya a sashen da kamfanin Triacta Nigeria Limited ke gudanarwa, inda ya ce kamfanin ya kai kashi 16 cikin 100 kacal na aiki duk da cewa an ba shi kwangilar a kusan lokaci guda tun Mayun 2023.

“Wannan hanya na da matuƙar muhimmanci. ‘Yan Najeriya na shan wahala. Hatsarori na yawaita, kuma tafiyar daga Sakkwato zuwa Gusau, wadda ya kamata ta ɗauki awa ɗaya da rabi, yanzu tana ɗaukar awanni huɗu zuwa biyar. Wannan ba abin yarda ba ne,” in ji Goronyo.

Ministan ya bayyana cewa lokacin kammala aikin gaba ɗaya an sa shi ne a shekarar 2028, inda ya sake jaddada ƙudirin Gwamnatin Tarayya na gina hanyoyi masu ɗorewa ta amfani da fasahar kankare mai ƙarfe, yana mai danganta lalacewar hanyoyin kwalta da yawan lodin manyan motoci.

A ziyarar, Ministan ya samu rakiyar wasu Daraktoci na Ma’aikatar Ayyuka, da kuma Kontarola na Ma’aikatar Ayyuka a Jihar Zamfara.

AMINU DALHATU

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci6 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara