Connect with us

Labarai

Rundunar ‘Yan Sanda ta Kebbi Ta Kama Dan Damfara

Published

on

Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Kebbi ta kama wani mutum mai suna Hamza Abdullahi Sama, mazaunin unguwar KCC a Birnin Kebbi, bisa zargin damfarar sama da mutum 175 da ke neman aikin yi, a ƙarƙashin hujjar samar musu da ayyukan shirin ciyar da ɗalibai a makarantu da gwamnatin jiha ta amince da su.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Bashir Usman, ne ya sanar da hakan yayin da yake yi wa manema labarai bayani a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

SP Bashir ya ce binciken da aka gudanar ya nuna cewa wanda ake zargin ya yi karya ta hanyar bayyana kansa a matsayin wanda Gwamnatin Jihar Kebbi ta bashi damar shirya daukar ma’aikata a makarantun firamare da sakandare.

Ya ce bisa wannan ƙaryar wakilci, waɗanda abin ya shafa—ciki har da Shafa’atu, Yusuf Yahaya, Hussaini Sani, Ubaida Abubakar, da sauransu sun yarda suka biya Naira dubu talatin kowanne, a matsayin kudaden kafin alkalami na wasu abubuwa kafin basu aikin.

SP Bashir ya ƙara da cewa ƙarin bincike ya tabbatar da cewa wanda ake zargin ya damfari jimillar Naira miliyan 5 da dubu 200 daga hannun waɗanda abin ya shafa, ta hanyar yaudara da gangan, domin babu irin waɗannan guraben aiki, kuma ba a ba shi izini daga kowace hukuma ta gwamnati ba don ɗaukar ma’aikata ko sarrafa ayyuka a madadinta.

A halin yanzu, wanda ake zargin na tsare a hannun ‘yan sanda, kuma bincike na ci gaba da gudana da nufin gurfanar da shi gaban kotu bayan kammala bincike. Rundunar ta kuma ja hankalin al’umma da su kasance masu faɗake da taka-tsantsan daga mutanen da ke cin moriyar halin ƙunci na masu neman aiki ta hanyar shirya aikin yi na bogi.

SANI DUTSINMA

Labarai

Labarai19 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara