Labarai
Rundunar ‘Yan Sanda ta Kebbi Ta Kama Dan Damfara
Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Kebbi ta kama wani mutum mai suna Hamza Abdullahi Sama, mazaunin unguwar KCC a Birnin Kebbi, bisa zargin damfarar sama da mutum 175 da ke neman aikin yi, a ƙarƙashin hujjar samar musu da ayyukan shirin ciyar da ɗalibai a makarantu da gwamnatin jiha ta amince da su.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Bashir Usman, ne ya sanar da hakan yayin da yake yi wa manema labarai bayani a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.
SP Bashir ya ce binciken da aka gudanar ya nuna cewa wanda ake zargin ya yi karya ta hanyar bayyana kansa a matsayin wanda Gwamnatin Jihar Kebbi ta bashi damar shirya daukar ma’aikata a makarantun firamare da sakandare.
Ya ce bisa wannan ƙaryar wakilci, waɗanda abin ya shafa—ciki har da Shafa’atu, Yusuf Yahaya, Hussaini Sani, Ubaida Abubakar, da sauransu sun yarda suka biya Naira dubu talatin kowanne, a matsayin kudaden kafin alkalami na wasu abubuwa kafin basu aikin.
SP Bashir ya ƙara da cewa ƙarin bincike ya tabbatar da cewa wanda ake zargin ya damfari jimillar Naira miliyan 5 da dubu 200 daga hannun waɗanda abin ya shafa, ta hanyar yaudara da gangan, domin babu irin waɗannan guraben aiki, kuma ba a ba shi izini daga kowace hukuma ta gwamnati ba don ɗaukar ma’aikata ko sarrafa ayyuka a madadinta.
A halin yanzu, wanda ake zargin na tsare a hannun ‘yan sanda, kuma bincike na ci gaba da gudana da nufin gurfanar da shi gaban kotu bayan kammala bincike. Rundunar ta kuma ja hankalin al’umma da su kasance masu faɗake da taka-tsantsan daga mutanen da ke cin moriyar halin ƙunci na masu neman aiki ta hanyar shirya aikin yi na bogi.
SANI DUTSINMA
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
