Labarai
Shugaban Kasa Zai Kai Ziyarar Aiki A TÜRKIYA
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai tashi daga Abuja a Litinin, 26 ga Janairu, domin kai ziyarar aikin ƙasa zuwa Jamhuriyar Türkiye.
Manufar ziyarar ita ce ƙarfafa kyakkyawar alaƙar da ke akwai tsakanin ƙasashen biyu, tare da binciko ƙarin hanyoyin haɗin gwiwa a fannoni da suka haɗa da tsaro, ilimi, bunƙasa zamantakewa, kirkire-kirkire da harkar sufurin jiragen sama.
Idan za a iya tunawa, Shugaban Ƙasar Türkiye, Recep Tayyip Erdogan, ya kai ziyarar aiki zuwa Najeriya daga 19 zuwa 20 ga Oktoba, 2021.
A yayin ziyarar Shugaba Tinubu, ƙasashen biyu za su gudanar da tattaunawar siyasa da diflomasiyya kan muhimman batutuwan bai ɗaya da suka shafi kuɗi da harkokin kasuwanci, sadarwa, cinikayya da zuba jari.
Ajandar ziyarar za ta haɗa da taron manyan jami’ai daga ɓangarorin biyu, tare da sa hannu kan yarjejeniyoyin fahimtar juna a fannoni kamar binciken kimiyya, makamashi, haɗin gwiwar fasaha, kafofin watsa labarai da sadarwa, haɗin gwiwar soja da ka’idoji, da sauransu.
Haka nan, za a gudanar da taron kasuwanci, wanda zai haɗa ’yan kasuwa da masu zuba jari daga ƙasashen biyu, domin gano damammakin haɗin gwiwa a lokutan ziyarar.
Ana sa ran Shugaba Tinubu zai dawo ƙasar nan bayan kammala ziyarar.
BELLO WAKILI
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai6 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
