Connect with us

Labarai

Shugaban Kasa Zai Kai Ziyarar Aiki A TÜRKIYA

Published

on

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai tashi daga Abuja a Litinin, 26 ga Janairu, domin kai ziyarar aikin ƙasa zuwa Jamhuriyar Türkiye.

Manufar ziyarar ita ce ƙarfafa kyakkyawar alaƙar da ke akwai tsakanin ƙasashen biyu, tare da binciko ƙarin hanyoyin haɗin gwiwa a fannoni da suka haɗa da tsaro, ilimi, bunƙasa zamantakewa, kirkire-kirkire da harkar sufurin jiragen sama.

Idan za a iya tunawa, Shugaban Ƙasar Türkiye, Recep Tayyip Erdogan, ya kai ziyarar aiki zuwa Najeriya daga 19 zuwa 20 ga Oktoba, 2021.

A yayin ziyarar Shugaba Tinubu, ƙasashen biyu za su gudanar da tattaunawar siyasa da diflomasiyya kan muhimman batutuwan bai ɗaya da suka shafi kuɗi da harkokin kasuwanci, sadarwa, cinikayya da zuba jari.

Ajandar ziyarar za ta haɗa da taron manyan jami’ai daga ɓangarorin biyu, tare da sa hannu kan yarjejeniyoyin fahimtar juna a fannoni kamar binciken kimiyya, makamashi, haɗin gwiwar fasaha, kafofin watsa labarai da sadarwa, haɗin gwiwar soja da ka’idoji, da sauransu.

Haka nan, za a gudanar da taron kasuwanci, wanda zai haɗa ’yan kasuwa da masu zuba jari daga ƙasashen biyu, domin gano damammakin haɗin gwiwa a lokutan ziyarar.

Ana sa ran Shugaba Tinubu zai dawo ƙasar nan bayan kammala ziyarar.

BELLO WAKILI

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci6 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara