Connect with us

Labarai

Kungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria 

Wata ƙungiyar al’umma mai suna Hadejia Advocacy ta yaba wa Gwamnan  Jigawa, Umar Namadi, kan yadda ya shiga tsakani a lamarin Walida wadda ake zargin wani jami’in Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) mai suna Ifeanyi Festus Onyewuenyi da yin garkuwa da ita.

Ƙungiyar ta bayyana cewa ceto yarinyar tare da jaririnta, waɗanda yanzu suke ƙarƙashin kulawar Gwamnatin Jihar Jigawa, wata babbar shaida ce da ke nuna ƙudirin Gwamna Namadi na kare rayuwa, mutunci da walwalar al’ummar jihar.

Shugaban ƙungiyar, Comrade Abubakar Babangida ne ya bayyana hakan yayin da yake jawabi a wani gangamin zanga-zangar goyon baya da aka gudanar a  garin Hadejia.

Comrade Abubakar ya sake jaddada kudirin ƙungiyarsu na ci gaba da mara wa gwamnatin Gwamna Namadi baya domin ganin an bi wannan shari’a har zuwa ƙarshe, tare da tabbatar da an yi wa waɗanda abin ya shafa adalci.

Sai dai masu zanga-zangar lumanar sun soki zanga-zangar da ƙungiyar ‘Hadejia Ina Mafita’ ta shirya, inda suka bayyana ta a matsayin wadda ke yaɗa bayanai marasa sahihanci da kuma ruɗar da jama’a, lamarin da ka iya haifar da rikici da hargitsi a cikin al’umma.

Sun kuma yi kira ga shugabannin Hadejia Ina Mafita da su riƙa yin taka-tsantsan yayin da suke magana ko sharhi kan irin waɗannan muhimman batutuwa, tare da gujewa siyasantar da su ko kuma ɓata sunan gwamnati.

Hakazalika, wata ƙungiyar mata mai suna Jigawa Women Development Initiative ta gudanar da zanga-zangar lumana a Dutse, babban birnin jihar, domin nuna farin cikinsu kan rawar da Gwamna Namadi ya taka a matsayin uba da jagora a lamarin Walida Abdullahi.

Ƙungiyar matan ta bayyana matuƙar damuwarta kan abin da ya faru, tare da nuna tausayi ga wadda abin ya shafa da iyayenta bisa irin mummunan cin zarafin da ake zargin wanda ake tuhuma ya yi mata.

Don haka sun yi kira ga al’umma gaba ɗaya da su haɗa kai wajen nuna goyon baya ga Gwamnatin Jihar Jigawa domin tabbatar da cewa an yi adalci ga Walida Abdullahi.

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci6 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara