Labarai
Ramadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
Daga Yusuf Zubairu Kauru
Sarkin Kauru da ke Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u Shehu Usman, ya yi kira da a kara inganta tsaro a yankin, inda ya bukaci hukumomi su rika sa ido sosai kan masu ba da bayanan sirri, tare da samar wa jami’an tsaro isasshen tallafi domin su gudanar da aikinsu yadda ya kamata.
Mai Martaba Sarkin ya bayyana hakan ne a yayin taron bude baki na watan Ramadan na shekara-shekara da ake gudanarwa a ranar 15 ga watan Ramadan a fadarsa da ke Kauru.
Sarkin ya kuma bukaci al’umma su kara dagewa da yin addu’o’i domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar nan, yana mai cewa manoma na fuskantar kalubale masu yawa sakamakon tashin farashin kayayyakin abinci, lamarin da ke shafar rayuwarsu da harkokin noma.
Ya kuma jaddada muhimmancin karfafa dankon zumunci musamman a wannan wata mai alfarma na Ramadan, tare da karfafa gwiwar jama’a da kungiyoyi su rika taimakawa marasa galihu ta hanyar bayar da abinci da sauran tallafi.

Makaman Kauru, Alh Umaru Abubakar

Hakazalika, Sarkin ya yabawa Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, kan ayyukan ci gaba da gwamnatinsa ke aiwatarwa wadanda ke kawo sauyi mai ma’ana ga al’ummomin Karamar Hukumar Kauru.
Daga karshe, ya bukaci mazauna yankin su ci gaba da bai wa jami’an tsaro hadin kai, tare da dagewa da yin addu’o’i domin samun dawwamammen zaman lafiya a fadin kasar nan.

Rediyon Najeriya Kaduna ta rawaito cewa Sarkin ya rufe taron da addu’o’in samun zaman lafiya da cigaba, tare da rokon Allah ya kara wa masarautar daukaka.
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci7 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
