Connect with us

Labarai

Ramadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu

Published

on

Daga Yusuf Zubairu Kauru

Sarkin Kauru da ke Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u Shehu Usman, ya yi kira da a kara inganta tsaro a yankin, inda ya bukaci hukumomi su rika sa ido sosai kan masu ba da bayanan sirri, tare da samar wa jami’an tsaro isasshen tallafi domin su gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

Mai Martaba Sarkin ya bayyana hakan ne a yayin taron bude baki na watan Ramadan na shekara-shekara da ake gudanarwa a ranar 15 ga watan Ramadan a fadarsa da ke Kauru.

 

Sarkin ya kuma bukaci al’umma su kara dagewa da yin addu’o’i domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar nan, yana mai cewa manoma na fuskantar kalubale masu yawa sakamakon tashin farashin kayayyakin abinci, lamarin da ke shafar rayuwarsu da harkokin noma.

Ya kuma jaddada muhimmancin karfafa dankon zumunci musamman a wannan wata mai alfarma na Ramadan, tare da karfafa gwiwar jama’a da kungiyoyi su rika taimakawa marasa galihu ta hanyar bayar da abinci da sauran tallafi.

 

Makaman Kauru, Alh Umaru Abubakar

Hakazalika, Sarkin ya yabawa Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, kan ayyukan ci gaba da gwamnatinsa ke aiwatarwa wadanda ke kawo sauyi mai ma’ana ga al’ummomin Karamar Hukumar Kauru.

Daga karshe, ya bukaci mazauna yankin su ci gaba da bai wa jami’an tsaro hadin kai, tare da dagewa da yin addu’o’i domin samun dawwamammen zaman lafiya a fadin kasar nan.

Rediyon Najeriya  Kaduna ta rawaito cewa Sarkin ya rufe taron da addu’o’in samun zaman lafiya da cigaba, tare da rokon Allah ya kara wa masarautar  daukaka.

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci7 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara