Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Bin Kadin Shari’ar Walida Abdulhadi

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria 

Gwamna Umar Namadi ya tabbatar da cewa Gwamnatin  Jigawa za ta bi sawun shari’ar sace ‘yar asalin jihar, Walida Abdulhadi, har zuwa ƙarshe, tare da tabbatar da an yi adalci.

Gwamnan ya bayar da wannan tabbaci ne a ranar Laraba lokacin da ya gana da iyayen Walida tare da lauyansu a Fadar Gwamnati da ke Dutse.

A yayin ganawar, gwamnan ya yi wa iyayen bayani kan halin da Walida ke ciki a halin yanzu, tare da jaddada ƙudirin gwamnati na tabbatar da kula da lafiyar ta, ci gaba da karatunta da kuma kula da walwalarta gaba ɗaya.

Ya bayyana cewa a halin yanzu Walida na karɓar kulawar jinya a wani asibiti da Gwamnatin Jigawa ke ɗaukar nauyin kuɗaɗensa, yana mai cewa bayan kammala wannan kulawa, za a mayar da ita cikin iyalanta.

Gwamnan ya kuma bayyana cewa an riga an tura ƙwararrun ma’aikatan kula da walwalar al’umma domin ba Walida da jaririnta kulawa ta musamman, yana mai jaddada cewa an tanadi dukkan matakan tallafi da suka dace domin kare lafiyarta da tabbatar da ganin ta murmure.

Bugu da ƙari, Gwamna Namadi ya ce gwamnatin jihar za ta mayar da Walida makaranta tare da ɗaukar nauyin karatunta gaba ɗaya domin ta ci gaba da neman ilimi ba tare da wata tangarda ba.

Da yake bayyana lamarin a matsayin satar mutane kai tsaye, gwamnan ya sha alwashin cewa gwamnatin jihar za ta tabbatar da an yi adalci ta hanyoyin shari’a da suka dace, kuma duk wanda aka samu da laifi za a hukunta shi bisa doka.

Haka kuma ya sanar da cewa gwamnati za ta tallafa wa Walida da iyalanta domin inganta rayuwarsu da taimaka musu su sake farfaɗo da rayuwarsu.

Gwamna Namadi ya sake nanata ƙudirin Gwamnatin Jihar Jigawa na kare haƙƙoƙi da mutuncin dukkan ‘yan jihar a duk inda suke.

Da yake magana a madadin iyayen Walida, lauyanta Barrista Kabiru Adamu ya gode wa Gwamna Namadi bisa saurin ɗaukar matakin ceto yarinyar da kuma ƙoƙarin gwamnati na ganin an dawo da martabar ta.

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci6 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara