Labarai
Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Bin Kadin Shari’ar Walida Abdulhadi
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamna Umar Namadi ya tabbatar da cewa Gwamnatin Jigawa za ta bi sawun shari’ar sace ‘yar asalin jihar, Walida Abdulhadi, har zuwa ƙarshe, tare da tabbatar da an yi adalci.
Gwamnan ya bayar da wannan tabbaci ne a ranar Laraba lokacin da ya gana da iyayen Walida tare da lauyansu a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
A yayin ganawar, gwamnan ya yi wa iyayen bayani kan halin da Walida ke ciki a halin yanzu, tare da jaddada ƙudirin gwamnati na tabbatar da kula da lafiyar ta, ci gaba da karatunta da kuma kula da walwalarta gaba ɗaya.
Ya bayyana cewa a halin yanzu Walida na karɓar kulawar jinya a wani asibiti da Gwamnatin Jigawa ke ɗaukar nauyin kuɗaɗensa, yana mai cewa bayan kammala wannan kulawa, za a mayar da ita cikin iyalanta.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa an riga an tura ƙwararrun ma’aikatan kula da walwalar al’umma domin ba Walida da jaririnta kulawa ta musamman, yana mai jaddada cewa an tanadi dukkan matakan tallafi da suka dace domin kare lafiyarta da tabbatar da ganin ta murmure.
Bugu da ƙari, Gwamna Namadi ya ce gwamnatin jihar za ta mayar da Walida makaranta tare da ɗaukar nauyin karatunta gaba ɗaya domin ta ci gaba da neman ilimi ba tare da wata tangarda ba.
Da yake bayyana lamarin a matsayin satar mutane kai tsaye, gwamnan ya sha alwashin cewa gwamnatin jihar za ta tabbatar da an yi adalci ta hanyoyin shari’a da suka dace, kuma duk wanda aka samu da laifi za a hukunta shi bisa doka.
Haka kuma ya sanar da cewa gwamnati za ta tallafa wa Walida da iyalanta domin inganta rayuwarsu da taimaka musu su sake farfaɗo da rayuwarsu.
Gwamna Namadi ya sake nanata ƙudirin Gwamnatin Jihar Jigawa na kare haƙƙoƙi da mutuncin dukkan ‘yan jihar a duk inda suke.
Da yake magana a madadin iyayen Walida, lauyanta Barrista Kabiru Adamu ya gode wa Gwamna Namadi bisa saurin ɗaukar matakin ceto yarinyar da kuma ƙoƙarin gwamnati na ganin an dawo da martabar ta.
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai6 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
