Kasuwanci
Gwamna AbdulRazaq Ya Yi Jimamin Kisan Jami’in Gandun Daji
Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa kan rasuwar wani jami’in gandun daji, Omotosho Olawuyi Samuel, wanda ya rasa ransa yayin artabu da wasu ’yan bindiga masu garkuwa da mutane a ƙauyen Koro, da ke Ƙaramar Hukumar Ekiti ta jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Rafiu Ajakaye, ya fitar, gwamnan ya yaba da jarumtaka da kishin ƙasa da jami’an gandun daji da ’yan sa-kai na tsaro na al’umma suka nuna, inda suka kai farmaki kan ’yan bindigar da ke tserewa.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa gwamnatin jihar za ta bayar da tallafin naira miliyan goma (₦10m) ga iyalan mamacin jami’in, a matsayin alamar godiya da jin daɗin gwamnati bisa sadaukarwar rayuwarsa.
Haka zalika, sanarwar ta miƙa ta’aziyya ga iyalan Omotosho Olawuyi Samuel da kuma abokan aikinsa da suka yi yaƙi tare da shi cikin jarumta.
ALI MUHAMMAD RABIU
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
