Kasuwanci
Coci-coci a Kurmin Walin Jihar Kaduna Sun Gudanar da Ibada Bayan Garkuwa da Mutane
An gudanar da ibadar Lahadi a ƙarƙashin tsauraran matakan tsaro a al’ummar Kurmin Wali da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna, biyo bayan garkuwa da mazauna 166 da ake zargin ‘yan bindiga ne suka yi a makon da ya gabata.
Ziyarar da Rediyo Nijeriya ta kai yankin ta nuna cewa yawan masu halartar ibada ya ragu ƙwarai a coci-coci uku da lamarin ya shafa, sakamakon yadda da dama daga cikin masu ibada ke cikin waɗanda aka sace, yayin da wasu kuma suka tsere daga yankin saboda fargabar sake kai hari. Yanayin ibadar ya kasance cike da jimami, inda aka fi mayar da hankali wajen yin addu’o’in dawo da waɗanda aka sace lafiya da kuma kawo zaman lafiya a yankin da ke fama da matsalar tsaro.
Da yake zantawa da wakilinmu, Sakataren Cocin Cherubim and Seraphim Church Two, Mista Jonathan Na’allah, ya ce babban abin da ke damun mambobin cocin shi ne lafiya da tsaron ‘yan uwansu da ke hannun masu garkuwa. Ya kara da cewa mazauna yankin na ci gaba da rayuwa cikin fargaba da tashin hankali sakamakon yawan faruwar sace-sace a al’ummar. Sai dai ya ce ganin jami’an tsaro a fili yayin ibadar ya dan ba masu ibada kwanciyar hankali.
An kuma gudanar da ibada ta haɗin gwiwa tsakanin Cocin ECWA da Cherubim and Seraphim Church One a wuri guda, inda mambobi suka yi addu’o’in neman taimakon Ubangiji da kuma nasarar kokarin gwamnati na shawo kan matsalolin tsaro da ke addabar yankin.
Shugabannin coci-cocin, Malam Danjuma Wali da Mista Yunana Adauji, sun yaba wa Gwamnatin Jihar Kaduna bisa alkawarin inganta ababen more rayuwa a yankin. Sai dai sun yi kira da a dauki mataki cikin gaggawa domin ganin an saki waɗanda aka sace, suna mai jaddada cewa al’ummar ba za ta koma rayuwa ta yau da kullum ba matuƙar har yanzu da dama na hannun ‘yan bindiga.
A halin yanzu, Gwamnatin Jihar Kaduna ta fara daukar matakai domin cika alkawuran da ta dauka na ababen more rayuwa, inda aka tura manyan motoci da injinan aiki zuwa hanyar da ke shiga al’ummar domin fara ayyukan ginata. Wannan ya biyo bayan alkawarin da Gwamna Uba Sani ya yi yayin ziyararsa Kurmin Wali jim kaɗan bayan faruwar lamarin garkuwa da mutane.
Mazauna yankin sun bayyana fatan alheri cewa dorewar aikin tsaro da kuma ayyukan ci gaba da aka yi alkawari za su taimaka wajen maido da kwarin gwiwa da zaman lafiya a al’ummar.
COV / Shindong Bala
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
