Connect with us

Kasuwanci

Coci-coci a Kurmin Walin Jihar Kaduna Sun Gudanar da Ibada Bayan Garkuwa da Mutane

Published

on

An gudanar da ibadar Lahadi a ƙarƙashin tsauraran matakan tsaro a al’ummar Kurmin Wali da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna, biyo bayan garkuwa da mazauna 166 da ake zargin ‘yan bindiga ne suka yi a makon da ya gabata.

Ziyarar da Rediyo Nijeriya ta kai yankin ta nuna cewa yawan masu halartar ibada ya ragu ƙwarai a coci-coci uku da lamarin ya shafa, sakamakon yadda da dama daga cikin masu ibada ke cikin waɗanda aka sace, yayin da wasu kuma suka tsere daga yankin saboda fargabar sake kai hari. Yanayin ibadar ya kasance cike da jimami, inda aka fi mayar da hankali wajen yin addu’o’in dawo da waɗanda aka sace lafiya da kuma kawo zaman lafiya a yankin da ke fama da matsalar tsaro.

Da yake zantawa da wakilinmu, Sakataren Cocin Cherubim and Seraphim Church Two, Mista Jonathan Na’allah, ya ce babban abin da ke damun mambobin cocin shi ne lafiya da tsaron ‘yan uwansu da ke hannun masu garkuwa. Ya kara da cewa mazauna yankin na ci gaba da rayuwa cikin fargaba da tashin hankali sakamakon yawan faruwar sace-sace a al’ummar. Sai dai ya ce ganin jami’an tsaro a fili yayin ibadar ya dan ba masu ibada kwanciyar hankali.

An kuma gudanar da ibada ta haɗin gwiwa tsakanin Cocin ECWA da Cherubim and Seraphim Church One a wuri guda, inda mambobi suka yi addu’o’in neman taimakon Ubangiji da kuma nasarar kokarin gwamnati na shawo kan matsalolin tsaro da ke addabar yankin.

Shugabannin coci-cocin, Malam Danjuma Wali da Mista Yunana Adauji, sun yaba wa Gwamnatin Jihar Kaduna bisa alkawarin inganta ababen more rayuwa a yankin. Sai dai sun yi kira da a dauki mataki cikin gaggawa domin ganin an saki waɗanda aka sace, suna mai jaddada cewa al’ummar ba za ta koma rayuwa ta yau da kullum ba matuƙar har yanzu da dama na hannun ‘yan bindiga.

A halin yanzu, Gwamnatin Jihar Kaduna ta fara daukar matakai domin cika alkawuran da ta dauka na ababen more rayuwa, inda aka tura manyan motoci da injinan aiki zuwa hanyar da ke shiga al’ummar domin fara ayyukan ginata. Wannan ya biyo bayan alkawarin da Gwamna Uba Sani ya yi yayin ziyararsa Kurmin Wali jim kaɗan bayan faruwar lamarin garkuwa da mutane.

Mazauna yankin sun bayyana fatan alheri cewa dorewar aikin tsaro da kuma ayyukan ci gaba da aka yi alkawari za su taimaka wajen maido da kwarin gwiwa da zaman lafiya a al’ummar.

COV / Shindong Bala

Labarai

Labarai19 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara