Connect with us

Labarai

Babban Hafsan Sojin Sama Ya Tattauna da Tsofaffin Sojoji a Kaduna

Published

on

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ta sake jaddada ƙudirin ta na inganta walwalar jami’anta, masu aiki da kuma waɗanda suka yi ritaya.

Babban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Sunday Aneke, ya bayar da wannan tabbaci ne a yayin taron shekara ta 2025 na tattaunawa tsakanin Babban Hafsan Sojin Sama da tsofaffin sojoji da ke zaune a Jihar Kaduna.

Air Marshal Sunday Aneke ya danganta nasarori da ci gaban da Rundunar Sojin Sama ta samu da ƙoƙari da sadaukarwar da tsofaffin sojoji suka yi a lokacin aikinsu.

Da yake wakiltar Babban Hafsan, Babban Jami’in Gudanarwa, Air Vice Marshal Anthony Martins, ya bayyana cewa domin girmama irin gudummawar da suka bayar, Rundunar Sojin Sama ta jajirce wajen kula da walwalarsu da jin daɗinsu gaba ɗaya.

A cewarsa, an tsara shirye-shiryen tallafin walwala na musamman domin tsofaffin sojoji, ba wai kawai don inganta rayuwarsu ba, har ma da ƙarfafa gwiwar jami’an da ke kan aiki, ta hanyar tabbatar musu cewa za a kula da su yadda ya kamata bayan ritaya.

Tun da farko, a jawabinsa na maraba, Kwamandan Rundunar Horar da Sojin Sama Air Vice Marshal Esen Efanga, ya bayyana cewa taron wata dama ce ta nazari kan ainihin ma’anar zama tsohon soja, tare da jaddada cewa Rundunar Sojin Sama da kuma Sojojin Ƙasa gaba ɗaya za su ci gaba da amfana da tarin gogewarsu.

A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar Walwalar Tsofaffin Sojoji, Malam Usman Yusuf mai ritaya, ya nuna matukar farin ciki, yana mai cewa taron zai taimaka matuƙa wajen inganta rayuwar tsofaffin sojoji.

Babban abin da ya dauki hankali a taron shi ne zaman tambaya da amsa kai tsaye, tare da shirye-shiryen kula da lafiya.

Usman Sani

Labarai

Labarai19 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara