Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai

Published

on

Daga Bello Wakili

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-baci kan harkar tsaro a duk fadin kasar, sakamakon karuwar kalubalen tsaro da ake fuskanta.

Shugaban ya ce za a dauki sabbin jami’an tsaro nan ba da jimawa ba, wadanda suka hada da na sojiin, ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro — domin karfafa matakan tsaron kasa.

A karkashin sabon umarnin, an bai wa Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ikon daukar karin jami’aaidubu ashirin,  wanda hakan zai kawo yawan sabbin  jami’an da za a dauka bana zuwa dubu hamsin.

Shugaban kasar ya kuma amince a yi amfani da sansanonin horas da matasa masu yi wa kasa  NYSC a matsayin wuraren horaswa na wucin gadi, sakamakon gyare-gyaren da ake yi a makarantun horar da ‘yan sanda a fadin kasar.

Haka zalika Jami’an da aka cire daga ayyukan tsaron manyan mutane za su samu horo na gaggawa kafin a tura su zuwa yankunan da ke da hadari.

Shugaban ya kuma bai wa Hukumar tsaro ta DSS umarnin gaggauta tura dakaru masu horo na musamman zuwa dazuka domin yaki da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga. A don haka, hukumar ta DSS za ta dauki karin ma’aikata don karfafa wannan aiki.

Shugaba Tinubu ya bukaci ‘yan Najeriya su bada hadin kai ga matakan tsaron da ake dauka.

Ya yaba wa jami’an tsaro bisa ceto daliban Jihar Kebbi 24 da aka yi garkuwa da su, da masu ibada 38 a Jihar Kwara, tare da tabbatar da cewa ana ci gaba da kokarin kubutar da daliban da aka yi garkuwa da su a Jihar Niger da sauran wadanda ke tsare.

Shugaban ya umurci Rundunar Soji ta kara zafafa ayyuka a dukkan yankunan da ake rikici, tare da jaddada muhimmancin ladabi, gaskiya da kin amincewa da cin hanci ko sakaci.

Ya mika ta’aziyya ga iyalan wadanda aka kashe a hare-haren da suka faru a Kebbi, Borno, Zamfara, Niger, Yobe da Kwara, tare da karrama jaruman sojojin da suka rasa rayukansu, ciki har da Birgediya-Janar Musa Uba.

Shugaba Tinubu ya sake tabbatar da goyon bayansa ga jami’an saro na jihohi, tare da kira ga Majalisar Dokoki ta Kasa da ta fara nazarin dokokin da za su bai wa jihohin da ke son kafa ‘yan sandan jiha damar yin hakan.

Ya shawarci gwamnatocin jihohi su sake duba tsarin kafa makarantun kwana a wuraren da ke da nisa ba tare da wadatattun matakan tsaro ba, sannan ya yi kira ga cibiyoyin addini su kara inganta tsaron wuraren ibada.

Dangane da rikice-rikicen manoma da makiyaya, Shugaban ya bukaci kungiyoyin makiyaya da su rungumi tsarin kiwo na zamani (ranching) tare da yin aiki tare da Gwamnatin Tarayya ta hannun sabuwar Ma’aikatar Raya Kiwo.

 

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara