Labarai
Gwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnatin Jihar Jigawa ta kara yin kira ga ‘yan kwangilar da aka baiwa sayen kayan abincin shan ruwa da su sanya tsoron Allah wajen sayen kayayyakin abinci masu inganci.
Shugaban kwamitin ciyarwar na watan Ramadan kuma Kwamishinan ma’aikatar ilimi matakin farko na jihar Dr Lawan Yunusa Danzomo ya yi wannan kiran a lokacin da ya ziyarci wasu cibiyoyin dafa abincin a yankin karamar hukumar Birnin kudu.
Ya bukace su da su sanya tsoron Allah wajen sayen kayayyakin abinci masu inganci da kuma tsafta kamar yadda aka cimma yarjejeniya da su da gwamnatin jihar.
Ya nuna gamsuwar sa dangane da yadda ake dafawa da raba abincin buda baki a cibiyoyin da aka tanadar a garuruwan Birnin Kudu da Kantoga da Kafin gana da Kangire dake karamar hukumar Birnin Kudu.
Dr Lawan Yunusa Danzomo wanda ya ziyarci cibiyoyin don ganewa idon sa yanda yawan abincin da tsaftarsa ya ke, ya nuna gamsuwarsa dangane da yadda wadanda aka baiwa alhakin aikin suke gudanar da rabon.

Yace Gwamnatin jihar Jigawa karkashin jagorancin Malam Umar Namadi ta bullo da shirin ciyarwar ne da nufin tallafawa dukkanin al’ummar jihar Jigawa musamman masu karamin karfi don su sami abin da za su yi buda baki da shi a lokacin shan ruwa.
A don haka, Dan Zomo ya yi kira ga yan kwangilar da su tabbatar suna sayen kayan abincin a yankunan da za a dafa don a karfafi tattalin arzikin al’ummar yankunan.
Yayi nuni da cewar, a kowacce cibiya ana dafa shinkafa da kunun tsamiya da kosai don rabawa mabukata har na tsawon watan Ramadan.
Kazalika, ya yi kira ga al’umma da su ci gaba da yi wa Gwamnati addu’oi ra musamman a wannan watan na Ramadan domin samun nasarar gudanar da aiyukan alherin da kuma zaman lafiya mai dorewa a fadin jihar Jigawa.
A jawaban su daban-daban, al’ummar garuruwan da kwamishinan ya ziyarta sun godewa gwamnatin jihar bisa bullo da shirin ciyarwar.
Sun kuma yi addu’ar fatan alkhairi ga Gwamna Umar Namadi da gwamnatin sa da ma jihar jigawa baki daya.
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci7 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
