Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin Jihar Jigawa ta kara yin kira ga ‘yan kwangilar da aka baiwa sayen kayan abincin shan ruwa da su sanya tsoron Allah wajen sayen kayayyakin abinci masu inganci.

Shugaban kwamitin ciyarwar  na watan Ramadan kuma Kwamishinan ma’aikatar ilimi matakin farko na jihar Dr Lawan Yunusa Danzomo ya yi wannan kiran a lokacin da ya ziyarci wasu cibiyoyin dafa abincin a yankin karamar hukumar Birnin kudu.

Ya bukace su da su sanya tsoron Allah wajen sayen kayayyakin abinci masu inganci da kuma tsafta kamar yadda aka cimma yarjejeniya da su da gwamnatin jihar.

Ya nuna gamsuwar sa dangane da yadda ake dafawa da raba abincin buda baki a cibiyoyin da aka tanadar a garuruwan Birnin Kudu da Kantoga da Kafin gana da Kangire dake karamar hukumar Birnin Kudu.

Dr Lawan Yunusa Danzomo wanda ya ziyarci cibiyoyin don ganewa idon sa yanda yawan abincin da tsaftarsa ya ke, ya nuna gamsuwarsa dangane da yadda wadanda aka baiwa alhakin aikin suke gudanar da rabon.

Yace Gwamnatin jihar Jigawa karkashin jagorancin Malam Umar Namadi ta bullo da shirin ciyarwar ne da nufin tallafawa dukkanin al’ummar jihar Jigawa musamman masu karamin karfi don su sami abin da za su yi buda baki da shi a lokacin shan ruwa.

A don haka, Dan Zomo ya yi kira ga yan kwangilar da su tabbatar suna sayen kayan abincin a yankunan da za a dafa  don a karfafi tattalin arzikin al’ummar yankunan.

Yayi nuni da cewar, a kowacce cibiya ana dafa shinkafa da kunun tsamiya da kosai don rabawa mabukata har na tsawon watan Ramadan.

Kazalika, ya yi kira ga al’umma da su ci gaba da yi wa Gwamnati addu’oi ra musamman a wannan watan na Ramadan domin samun nasarar gudanar da aiyukan alherin da kuma zaman lafiya mai dorewa a fadin jihar Jigawa.

A jawaban su daban-daban, al’ummar garuruwan da kwamishinan ya ziyarta sun godewa gwamnatin jihar bisa bullo da shirin ciyarwar.

Sun kuma yi addu’ar fatan alkhairi ga Gwamna Umar Namadi da gwamnatin sa da ma jihar jigawa baki daya.

 

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci7 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara